Gwamnan Osun Ademola Adeleke ya fice daga jam’iyyar PDP

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar PDP, wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da rikicin cikin gida a jam’iyyar ke kara karuwa.

Adeleke ya sanar da hakan ne ta shafinsa na X a daren Litinin, inda ya wallafa kwafin takardar murabus dinsa mai dauke da kwanan wata 4 ga Nuwamba, 2025.

A cikin takardar, Adeleke ya bayyana rikicin da ke faruwa a jam’iyyar a matsayin dalilin ficewarsa.

Ya rubuta cewa: “Sakamakon rikicin da jam’iyyar ke fama da shi, na yanke shawarar ficewa daga cikinta daga yau.”

Gwamnan ya gode wa jam’iyyar bisa damar da ta bashi ya yi aiki a matsayin Sanata mai wakiltar Osun West (2017–2019) da kuma Gwamnan jihar Osun.

Adeleke dai bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba bayan barin PDP.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com