Home Labarai Gwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan Siyasa

Gwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan Siyasa

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya cire Sunusi Surajo Kwankwaso daga mukamin mai ba shi shawara kan harkokin siyasa tare da maye gurbinsa da Mustapha Buhari Bakwana.

Hakan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran Gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Idan za’a iya tunawa Sunusi Surajo Kwankwaso ya bayyana cewa ya kai takardarsa ta ajiye aiki amma anki karbar, wanda ya ce hakan ce tasa a fito fili ya fadawa Duniya cewa ya ajiye mukamin nasa.

Sunusi Surajo Kwankwaso dai na daga cikin wadanda tun a tashin fari suka nuna cewa za su kasance tare da madugun Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Wannan dambarwar dai ta Sami asali ne tun lokacin da aka fara jita-jitar gwamnan Kano zai raba gari da ubangisansa na Siyasa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Bakwana dai ya taba rike wannan mukamin lokacin mulkin Dr. Abdullahi Umar Ganduje yana gwamnan Kano.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp