Home Taska ‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum...

‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar Kebbi

‘Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami’an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar Kebbi

Wasu ’yan bindiga sun kai hari garin Tsamiya da ke Ƙaramar Hukumar Bagudo a Jihar Kebbi, inda suka ƙone shingen bincike na rundunar Sibil Difens (NSCDC), tare da lalata wasu gine-gine a yankin.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar sun kuma yi garkuwa da wani mutum mai suna Alhaji Yusuf Bazamfare yayin harin da suka kai a ranar Asabar.

A cewar mazauna yankin, ’yan bindigar sun kuma ƙone gidan karuwai da kuma gidan wani mutum mai suna Sule Mai Goge sannan suka tsere.

Mai magana da yawun Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, SP Bashir Usman, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce rundunar ta tura jami’anta zuwa yankin nan take bayan samun rahoton harin.

Ya ce Kwamishinan ’yan sandan jihar ya bayar da umarnin tura ƙarin jami’an tsaro domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma a yankin.

“An fara bincike kan lamarin, sannan ana ƙoƙarin gano inda aka kai wanda aka yi garkuwa da shi domin kuɓutar da shi,” in ji shi.

SP Bashir Usman ya kuma buƙaci mazauna yankin da su kwantar da hankali tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kai da sahihan bayanai da za su taimaka wajen gudanar da aikin ceto da bincike.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 
X whatsapp