Home Taska Ƙasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar Sokoto

Ƙasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar Sokoto

Ƙasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar Sokoto

Ƙasurgumin ɗan bindigar nan, Bello Turji, ya bayyana a wani sabon bidiyo, inda ya ɗauki alhakin kisan wasu dakarun sojoji a Jihar Sakkwato.

Lamarin ya faru ne bayan da sojoji suka tashi zuwa garin Bargaja da ke Ƙaramar Hukumar Isa, sakamakon harin ’yan bindiga suka kai da sanyin safiyar ranar Asabar.

Mazauna yankin sun ce ’yan bindiga sun kai farmakin ne tsakanin ƙarfe 12:30 na dare zuwa 3 na safe, inda suka riƙa harbe-harbe, lamarin da ya jefa jama’a cikin tsoro.

Yayin da sojoji ke kan hanyar zuwa wajen domin kai ɗauki, wani bam da aka dasa a kan hanya ya tarwatsa motarsu a hanyar Isa zuwa Bargaja.

Rahotanni sun ce aƙalla sojoji biyu ne sun rasa rayukansu, yayin da wasu da dama suka jikkata.

A cikin bidiyon da ya fitar bayan aukuwar harin, Turji, ya ce yana murna da mutuwar abokan gabansa.

Ya kuma yi iƙirarin cewa mutanensa sun samu nasara a kan jami’an tsaro tare da ƙwato dabbobin da aka ƙwace a wajensu.

Rahotanni kuma sun nuna cewa an shiga damuwa a yankin kan cewa Turji na ƙara samun ƙarfi da kuma samun sabbin makamai a yankin iyakar Sakkwato da Zamfara.

Wani mai rajin kare haƙƙin jama’a, Basharu Altine Guyawa Isa, ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa Turji da wasu kwamandojinsa suna tara mayaƙa tare da horar da su.

Ya kuma ce wasu mayaƙa masu alaƙa da Boko Haram sun shiga cikin ƙungiyar domin taimakawa wajen horo da kuma kai hari.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar ta samu makamai masu hatsari ciki har da na’urar gani cikin dare.

Hukumomi ba su tabbatar da waɗannan zarge-zarge ba, kuma ’yan sandan Jihar Sakkwato ba su mayar da martani ba lokacin da aka nemi jin ta bakinsu.

Waɗannan rahotanni na ƙara haifar da fargaba a tsakanin mazauna wasu yankuna na Jihar Sakkwato da kewaye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƙasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar SokotoMasu Iƙirarin Jihadi Sun Hallaka Manoma 11 a Jihar Borno 'Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami'an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar KebbiTaron NUJ: Lokacin Da Manyan Jami’an Tsaro Suka Guji Yan Jarida Daga Yushau A. ShuaibSamar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar KatsinaZaben 2027: NDC ta Tsayar da Ɗan Kwankwaso Mataimakin ɗan Takarar Gwamnan KanoKotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher Musa
X whatsapp