Home SIYASA Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na...

Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam’iyyar NDC 

Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam’iyyar NDC 

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NDC, Peter Obi ya zargi Gwamnatin Tarayya da ƙulla maƙarƙashiyar hana shi yin takara a zaɓen shekarar 2027.

Yayin da yake jawabi a wani shirin horas da shugabanci da Ƙungiyar ‘NextGen Mentorship and Leadership Initiative‘ ta shirya a Jami’ar Madonna da ke Okija a Jihar Anambra ranar Juma’a, Obi ya yi iƙirarin cewa ana yin iƙirarin dakatar da shi daga shiga zaɓe mai zuwa.

“Idan na gaya muku abubuwan da nake fuskanta a yau, ba za ku ganni a nan ba. Mutane sun tambaye ni, ‘Shin har yanzu za ka je Madonna?’ Sai na ce, ‘Eh. Zan je.’ Suka ce da duk abubuwan da ke faruwa a Najeriya, har yanzu za ka je can, sai na ce, ‘Eh. Na ga mafi muninsa.’ A yau, Gwamnatin Tarayyar Najeriya tana yin duk mai yiwuwa don tabbatar da cewa ban zama ɗan takara a wannan zaɓen ba, amma ina gaya muku cewa ba za su yi nasara ba.”

“Idan kana rayuwa a inda babu ƙalubale, to ba ka rayuwa ne. Kada ku kalli ƙalubale, ƙalubale za su kasance a koyaushe. Ni ba ƙalubale nake kallo ba, burina shi ne inda na dosa. Na fi mayar da hankali ne kan sakamako mai kyau na inda na dosa, kuma hakan shi ne abin da yake ba ni ƙwarin gwiwa,” in ji shi.

Haka kuma Obi ya ƙalubalanci dukkan masu neman takarar shugaban ƙasa, ciki har da Shugaba Bola Tinubu, da su fito muhawarar bainar jama’a kan tsare-tsaren da suke da shi ga ƙasar.

“Ina ƙalubalantar duk wani mai takara da ya fito mu yi muhawara don ya faɗi abin da yake son yi wa wannan ƙasa, ciki har da Shugaba Bola Tinubu. Ba don na faranta muku rai nake faɗin hakan ba, a’a, don a canza Najeriya kuma a gyara ta,” in ji shi.

Tsohon Gwamnan na Jihar Anambra ya shaida wa ɗaliban cewa ba burin kansa ba ne yake yi, a’a, don muradin ganin ƙasar ta gyaru ne.

Haka kuma Obi ya yi tsokaci game da hukuncin Babbar Kotun Tarayya wadda ta soke wani hukunci na baya da ke umartar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta yi rajistar Jam’iyyar NDC a matsayin jam’iyyar siyasa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wata Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta soke hukuncinta na baya wanda ya umarci INEC da ta yi rajistar NDC a matsayin jam’iyyar siyasa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp