Home DUNIYA Kashi 80 Cikin 100 na Mutanen Afirka ba a yi Musu Allurar...

Kashi 80 Cikin 100 na Mutanen Afirka ba a yi Musu Allurar Rigakafin Corona ba – Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya

Kashi 80 Cikin 100 na Mutanen Afirka ba a yi Musu Allurar Rigakafin Corona ba – Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya

 

Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce kashi 80 cikin 100 na mutanen Afirka har yanzu ba a yi musu allurar riga-kafin corona ko da ɗaya ba.

Dr Tedros ya bayyana hakan ne a lokacin wani taro ta intanet yayin cika shekara daya da kaddamar da shirin samar da rigakafin a duniya da ake kira Covax.

Ya ce “kiyasinmu ya nuna cewa riga-kafin da za a samar za ta isa a yi wa dukkanin manya na duniya kuma har a kara yi wa mutanen da ke cikin hadarin kamuwa da cutar sosai zuwa wata uku na farkon shekaran nan”.

Covax shiri ne na tabbatar da raba daidai a tsakanin kasashen duniya wajen samar da riga-kafin corona.

Shugaban na WHO ya ce shirin ya gamu da nakasu sosai saboda abin da ya kira “kaka-gida” da kasashe suka yi a kan rigakafin da kuma yadda kamfanonin da ke samar da ita suka fi bayar da fifiko ga kasashe masu karfin arziki.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp