Home Labarai E-TICKETING: Gwamnatin Tarayya ta Sami Karin Miliyan 3 na Harajin Jirgin Kasa

E-TICKETING: Gwamnatin Tarayya ta Sami Karin Miliyan 3 na Harajin Jirgin Kasa

Ministan Sufuri Rotimi Amaechi yace an dakatar da Hukumar Lura da Sufurin Jiragen Kasa ta Nijeriya (NRC) daga sayar da tikitin hawa Jirgin ga matafiya.

Ya bayyanna hakan ne yayin da yake gabatar da takardar sahelewar saida tikitin da za’a sayar ta yanar gizo (E-ticketing) na Legas zuwa Ibadan dana Itakpe zuwa Warri ga hukumar ICRC

Ameachi Yace an dauki wannan mataki ne domin dakile cin hanci da rashawa da kuma barazanar rashin tsaro da Hukumar ta NRC ke fuskanta.

Ya kara da cewa tun bayan kaddamar da wannan tsari na E-Ticketing kudin shigar da ake samu ya rubanya.

PRNigeria ta rawaito Ameachi na cewa daukar wannan mataki ya zama waji ne kasancewar yadda matsalar rashin tsaro ke kara addabar hanyoyi a Nijeriya

“Duk da dai baza mu iya magance matsalar rashin tsaron da cin hanci da rashawa dari bisa dari ba, amma hakan zai rage matsalar rashin tsaron da muke fuskanta”

“yanzu gwamnatin Tarayya taga Alfanun wannan tsari, ta hanyar kara samun kudin shiga daga miliyan dari daya duk wata zuwa miliyan dari 4.”

Idan za’a iya tunawa PRNigeria ta rawaito cewa wasu ‘Yan Bindiga sun dasa abun fashewa a kan titin jirgin kasa daga Abuja zuwa kaduna Abinda yayi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da batan wasu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp