Home Labarai Majalisar Wakilan Nijeriya ta Bukaci Karin Girke Karin Jami’an Tsaro a Jihar...

Majalisar Wakilan Nijeriya ta Bukaci Karin Girke Karin Jami’an Tsaro a Jihar Taraba

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci Hafsan Sojin kasar da Babban Sifeto Janar su kara girke dakaru a jihar Taraba.

Da yake Karin haske kan kisan da ‘Yan bindiga suka yi a jihar yayin da yake gabatar da kudirin a zaman majalisar na ranar 10 ga watan Mayu, Dan Majalisa daga Jihar Taraba Usman Danjuma yace ‘Yan Bindiga yayin wani hari da ‘Yan Bindigar suka kai tsakar dare sun halaka Al’ummar kauyen da dama.

Mafi yawan Mazauna Kauyen na Tati dai manoma ne, sai dai harin na ‘yan bindiga ya tarwatsasu.

“sakamakon kiraye-kiraye neman dauki da mazauna kauyen suka yi, jami’an tsaro sun yi tattaki zuwa yankin inda ‘yan ta’addan suka yi musu kwantan bauna, inda suka halaka sojoji da shida.

Wannan dai na zuwa ne bayan da ‘yan bindiga suka halaka wani jami’in Dan sanda da wani farar hula a shingen ababen hawa, inda kwamanda bataliya ta 93 yayi batan dabo yayin gudanar da atisayen kawar da ‘Yan Ta’addan.

“an kai korafe-korafe ga jami’an tsaro kan yadda ‘yan bindigar ke zirga-zirga a kauyen a makonnin da suka gabata.

“ wannan ce ta sanya jami’an tsaron Musamman bataliya ta 93 da wasu Karin dakarun hadin gwuiwa, suka farwa ‘yan Ta’addan tare da samun nasarar kwace muggan makamai a hannun su.”

Dan majalisar ya nuna damuwar sa matuka kan yadda ‘yan bindigar ke sake kwarara yankunan Nijeriyar.

Yayin da majalisar ke amincewa da kudirin ta yi kira ga Hukumar Bada Agaji Gaggawata NEMA ta gaggauta kai Agaji ga Al’ummar da abin ya shafa a karamar hukumar Takum ta jihar Taraba.

Da yake ganawa da manema labarai, Danjuma yace ‘yan bindiga sun fito ne daga jihar Borno da jihar Plateau.

“Muna fuskantar babban kalubalen tsaro daga ‘yan bindiga a kudancin jihar Taraba, an kashe sama da mutane 42 cikin kwanaki 3 da suka gabata tare da kone gidaje 6 a karamar hukumar takum, kuma muna zargin ‘yan bindigar sun fito ne daga jihohin Filato da Borno.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp