Kwanaki Da Kai Hari Garin Owo, ‘Yan Bindiga Sun Sake Halaka Mutum 6 A Jihar Ondo.

Wasu ‘yan bindiga sun harbe a kalla mutum 6 a unguwar Sabo dake garin Ondo, a jihar Ondo a daren laraba.

Wannan dai na zuwa ne sa’oi 72 bayan wani harin ta’addanci da aka kai kan mujami’ar St. Francis catholic Church, a garin Owo inda suka halaka mutum 40, yayin da mutune da dama suka sami muggan raunuka.

An ruwaito cewa maharan saman Babura suka kai harin, duk da cewa wata majiya ta bayyanawa PRNigeria cewa sai da suka yiwa wasu mazauna yankin fashi kafin su tafi.

Kakakin rundnar ‘yan sandan Jihar Uwar gida Funmilayo Odunlami, ta tabbatar da faruwar lamarin, said ai tace ayyukan fashi ne da makami ba ‘yan bindiga, amma tuni jami’an hukumar suka bi sahu domin daukar matakan da suka dace.

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 16 hours 22 minutes 14 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 18 hours 3 minutes 39 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com