Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Sami Nasarar Kame Wasu ‘Yan Fashi

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Sami Nasarar Kame Wasu ‘Yan Fashi

Dakarun Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano dake Arewacin Nijeriya ta sami nasarar kame wasu matasa da take zargi da ayyukan fashi da makami a gidan wani dan Indiya dake jihar,

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ANIPR, wadda kaka raba ga manema labarai, sanarwa tace dakarun hukumar na Kan Kace Kwabo Wato (Operation Puff Adder), bisa jagorancin baturen ‘Yan sanda dake lura da shiyyar sharada a karamar hukumar Birnin da kewaye na jihar, sun sami wani bayanin sirri, kuma basuyi kasa a gwuiwa ba suka shiga aiki gadangadan, nan suka sami nasarar kame guda cikin wadanda ake zargin a cikin wani babur din Adaidaita Sahu a kofar gidan Dan Indiyan.

Kiyawa yace ko da matukin babur Din mai suna Alh. Musa Mai kimanin shekara 45 dan unguwar Tudun Rubudi ya hangi dakarun ‘yan sanda yayi yunkurin ranta a na kare, said ai dakarun Yan sanda sun harbi tayar Babur din nasa.

Matukin babur din da wani matashi Onyekachi Jude mai kimanin shekaru 19 dan Unguwar Rinji, a jihar kano, sun shiga hannun dakarun ‘yan sandan, sai dai Harbin da dakarun ‘yan Sanda sukayi tun da fari yaja hankalin ‘yan fashin dake cikin Gidan Dan Indiya nan sukayi kokarin guduwa, a kokarin nasu na guduwa dakarun ‘yan sandan sun sami nasarar kamei i). Moses Jude, dan shekara 23, dan unguwar Rinji,
da Sunday Titus, mai kimanin shekaru 20 dan unguwar Zoo Road Kano
sai  Kyunle Bhago, mai kimanin shekaru 22 a duniya dan Sabuwar Gandu duk a jihar ta Kano.

 

 

Sanarwar tace tun a binciken farko da aka gudanar kan wadanda ake zargin sun amsa cewa Musa ya zauna a gidan a baya, inda suka hada baki da wasu mutane uku kuma suka je gidan dan kasar Indiya a lokuta da dama, sai yayin da ‘yan sandan suka yi musu kofar rago guda cikin su ya tsere da wayar salula ta kimanin Naira Dubu 50 da kudi kimanin Dala, amma an sami damar kwato kayayyaki a hannun barayin da suka hadar da wayar kirar Honor, wuka mai kaifin, Takunkumin badda bami, da Na’urar shiga Yanar gizo ta Modem, sai kuma kudin kasar Indiya da yaka Rufi 550 da kuma wata jakar takardu.

Kakakin yace tuni Kwamshinan Sama’ila Shu’aibu Dikko, fsi ya bada umarnin yin bincika kan wadanda ake zargi inda daga bisani za’a mikasu gaban kuto domin yin abinda ya dace.

SP ABDULLAHI HARUNA KIYAWA, ANIPR,
POLICE PUBLIC RELATIONS OFFICER,
FOR: *COMMISSIONER OF POLICE, KANO STATE COMMAND.*

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp