Home Labarai Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Sami Nasarar Kame Wasu ‘Yan Fashi

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Sami Nasarar Kame Wasu ‘Yan Fashi

Dakarun Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano dake Arewacin Nijeriya ta sami nasarar kame wasu matasa da take zargi da ayyukan fashi da makami a gidan wani dan Indiya dake jihar,

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ANIPR, wadda kaka raba ga manema labarai, sanarwa tace dakarun hukumar na Kan Kace Kwabo Wato (Operation Puff Adder), bisa jagorancin baturen ‘Yan sanda dake lura da shiyyar sharada a karamar hukumar Birnin da kewaye na jihar, sun sami wani bayanin sirri, kuma basuyi kasa a gwuiwa ba suka shiga aiki gadangadan, nan suka sami nasarar kame guda cikin wadanda ake zargin a cikin wani babur din Adaidaita Sahu a kofar gidan Dan Indiyan.

Kiyawa yace ko da matukin babur Din mai suna Alh. Musa Mai kimanin shekara 45 dan unguwar Tudun Rubudi ya hangi dakarun ‘yan sanda yayi yunkurin ranta a na kare, said ai dakarun Yan sanda sun harbi tayar Babur din nasa.

Matukin babur din da wani matashi Onyekachi Jude mai kimanin shekaru 19 dan Unguwar Rinji, a jihar kano, sun shiga hannun dakarun ‘yan sandan, sai dai Harbin da dakarun ‘yan Sanda sukayi tun da fari yaja hankalin ‘yan fashin dake cikin Gidan Dan Indiya nan sukayi kokarin guduwa, a kokarin nasu na guduwa dakarun ‘yan sandan sun sami nasarar kamei i). Moses Jude, dan shekara 23, dan unguwar Rinji,
da Sunday Titus, mai kimanin shekaru 20 dan unguwar Zoo Road Kano
sai  Kyunle Bhago, mai kimanin shekaru 22 a duniya dan Sabuwar Gandu duk a jihar ta Kano.

 

 

Sanarwar tace tun a binciken farko da aka gudanar kan wadanda ake zargin sun amsa cewa Musa ya zauna a gidan a baya, inda suka hada baki da wasu mutane uku kuma suka je gidan dan kasar Indiya a lokuta da dama, sai yayin da ‘yan sandan suka yi musu kofar rago guda cikin su ya tsere da wayar salula ta kimanin Naira Dubu 50 da kudi kimanin Dala, amma an sami damar kwato kayayyaki a hannun barayin da suka hadar da wayar kirar Honor, wuka mai kaifin, Takunkumin badda bami, da Na’urar shiga Yanar gizo ta Modem, sai kuma kudin kasar Indiya da yaka Rufi 550 da kuma wata jakar takardu.

Kakakin yace tuni Kwamshinan Sama’ila Shu’aibu Dikko, fsi ya bada umarnin yin bincika kan wadanda ake zargi inda daga bisani za’a mikasu gaban kuto domin yin abinda ya dace.

SP ABDULLAHI HARUNA KIYAWA, ANIPR,
POLICE PUBLIC RELATIONS OFFICER,
FOR: *COMMISSIONER OF POLICE, KANO STATE COMMAND.*

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp