Dan Bindiga 1 Ya Mutu ‘Yan Sanda Sun Kama 3 A Jihar Benue

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Benue sun sami nasarar kame wasu da ake zargin na da hannu a kai harin garin Igama na karamar hukuma Okpokwu dake jihar.

ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar yan sandan jihar Catherine Anene ya fita a ranar Alhamis, yace wadanda ake zargin dai ya mutu ne sakamakon raunin harbi da ya samu a gwamzawar da jami’an ‘yan sandada gugun ‘yan bindigar.

Wakilin mu ya rawaito mana cewa maharan sun afka garin a yammacin ranar lahadi inda suka halaka mutum 15, daga bisani suka banka wuta a gidajen Al’ummar garin.

Ta cikin sanarwa rundunar ‘yan sandan ta tabbatar da jibge jami’anta hadin gwuiwa da sauran jami’an tsaro, domin bincika lungu da sako na dazukan dake yankin.

“A ranar 15 ga watan Yuni, misalin karfe 5 na safe, maharan dake makale a cikin daji, sun yi artabu da ‘yan sanda wanda ya kai ga an cafke Umar Nuhu, Dauda Alhaji, Musa Dako da Umaru Alhaji Sale.

“Daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Musa Dako ya samu raunuka kuma an kwantar da shi a Asibitin St. Mary’s dake Okpoga inda a karshe ya mutu.

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 12 hours 2 minutes 14 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 43 minutes 39 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com