Home Labarai Majalisar Wakilai ta Bukaci Buhari Ya Ceto Sauran Mutum 51 Dake Hannun...

Majalisar Wakilai ta Bukaci Buhari Ya Ceto Sauran Mutum 51 Dake Hannun ‘Yan Ta’adda

Train attack: Reps ask Buhari to secure release of remaining 51 kidnapped victims

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci shugaban kasar Muhammadu Buhari daya gaggauta daukar matakin ganin an sako sauran fasinjoji 51 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a a wani yarin jirgin kasan Abuja zuwa Kano.

Har ila yau, majalisar ta bukaci gwamnatin tarayya ta kafa wani kwamiti mai karfi don ganin an kubutar da wadanda ke hannun ‘yan bindigar, dadukkan wadanda ke hannun ‘yan bindigar a fadin kasar, gami da bayar da taimako ga iyalan wadanda aka yi garkuwa da su.

Wanna bukata ta majalisar ta biyo bayan Nazari kan wani kudiri da Bamidele Salam da wasu ‘yan majalisar su 10 suka gabatar a zauren majalisar.

PRnigeria ta rawaito Dan majalisar Salam Ya gudanar da wani tattaki shi kadai a kwaryar birnin tarayya, wanda ya bukaci a sako wadanda akayi garkuwa dasu.

Cikin kudirin, dan majalisar ya bayyana cewa sashe na 14 (2) (b) na kundin tsarin mulkin da aka yiwa kwaskwarima 1999, ya bayyana cewa, tsaro da jin dadin jama’a shi ne babbar manufar gwamnati, kamar yadda sashe na 17 (2) (b) na kundin tsarin mulkin kasar ya bayyana muhimmancin dan Adam tare da inganta martabar sa da kare ta.

Ya kara da cewa, tsawon shekaru 10 da suka wuce, ta’addanci, ‘yan fashi masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, gami da munana laifuka sun zamo annoba ga tsaron kasar a sassa daban-daban na kasar.

Da take amincewada kudirin, majalisar wakilan ta umarci dukkanin kwamitocin da abin ya shafa na majalisar da su tabbatar da aiki da kudirin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp