Home Labarai Majalisar Wakilan Nijeriya ta Zargi NNPC Da Badakalar Dala Biliyan 10 Na...

Majalisar Wakilan Nijeriya ta Zargi NNPC Da Badakalar Dala Biliyan 10 Na Tallafin Man Fetur

Majalisar wakilan Nijeriya ta yi zargin cewa an sace sama da Dalar Amurka Biliyan 10 na danyen man fetur, ta hanyar badakalar tallafin Man wanda kamfanin man fetur na kasar NNPC da sauran masu ruwa da tsaki a kamfanin su ka yi.

Don haka majalisar ta kafa wani kwamitin wucin gadi da zai binciki tsarin tallafin man fetur tsakanin shekarar 2017 zuwa 2021 da ga kamfanin na NNPC ya yi.

Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin da Dan majalisa mai wakiltar Edo Sergious Ogun ya shigar gaban majalisar a ranar laraba a birnin tarayya Abuja.

Ta cikin kudirin nasa, Mista Ogun yace an sanar da shi cewa a shekarar 2002, kamfanin na NNPC ya sayi danyen mai a farashin kasuwannin duniya, wanda ya kai ganga 445,000 a ko wacce rana.

Ya kara da cewa anyi hakan ne domin bada damar samar da man da ake amfani da shi a cikin gida, amma abin damuwar shine yadda a shekarar 2002 matatun man Nijeriya ke samar da ganga 445,000 a kowacce rana.

Sai dai kuma yace daga bisani karfin matatun ya ragu zuwa sifili sakamakon rashin inganci da kuma zargin cin hanci da rashawa ga masu ruwa da tsaki ya durkusar da fannin.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp