Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Jihar Niger

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Jihar Niger

Akalla fararen hula mutum 43 ne suka mutu wanda suka hadar da sojojin 30 da ‘yan sandan kwantar da tarzo 7 sakamakon harin ‘yan bindiga a wani wurin hakar ma’adanai  a karamar hukumar Shiroro dake jihar Nijer, kamar yadda wata majiya ta shaida mana.

A yayin da gwamnatin jihar ta Niger ke tabbatar da faruwar harin, ta bayyana cewa bata kai ga gano adadin wadanda harin ya rutsa dasu ba.

Mazauna yakin sun bayyana cewa jami’an Bincike sun gano gawarwakin sojoji da Jami’an ‘yan sandan 37 yashe a cikin daji ranar Alhamis, gami da gawarwakn fararen hula 6 duk a cikin dajin.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da ‘yan Nijeriya da ‘yan kasar Sin (Chaina) da dama a yayin harin da suka kai wajen hakar ma’adanan a ranar laraba.

Yusuf Kokki, wanda gudana ne cikin shuwagabannin kungiyar Matasan Shiroro, ta cikin wata sanarwa da ya aikewa manema labarai yace mazauna wurin sun shaida harin maharan dauke da muggan makamai.

Ya tabbatar da cewa lamarin ya faru ne yayin da ‘yan bindigar suka yiwa wurin hakar ma’adanan tsinke, nan suka fara harbi kan mai uwa da wabi akan ma’aikatan da masu tsaron lafiyar su.

Ya ce mazauna yankin zasu zakulo Karin wasu gawarwakin a aikin da suke cigaba da yi na nemo wadanda harin ya rutsa dasu.

Yace jami’an ‘yan sandan kwantar da tarzoma 7 sun mutu da wasu Karin fararen hula guda 6 a wajen hakar ma’adanan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp