Home Labarai Bagudu: Najeriya na Bukatar Masu Zuba Jari a Duniya don Habaka Tattalin...

Bagudu: Najeriya na Bukatar Masu Zuba Jari a Duniya don Habaka Tattalin Arziki

Gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu ya ce Najeriya na bukatar hadin gwiwar zuba jari a duniya domin gina tattalin arzikinta, inda ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa masu fata na gari duk da kalubalen da kasar ke fuskanta.

Bagudu ya hori ‘yan kasar da kada su yanke kauna ko kuma su karaya game da yadda basussukan kasar ke ciki wanda ka iya zama dalilin da zai sa Al’ummar kasar su yanke tsammani.

Hakan ya zo ne a daidai lokacin da takwaransa na jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya shawarci gwamnan jihar Ekiti mai jiran gado, Biodun Oyebanji, da ya inganta ci gaba ta hanyar gina gadon magabacinsa.

Gwamnonin sun yabawa gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi bisa yadda ya samar da amana tsakaninsa da mutanen Ekiti, ta hanyar gudanar da kyakkyawan shugabanci da ya shafi kowane bangare na tattalin arziki.

Sun yi magana ne a Ado Ekiti, jiya a wani taron kasa da kasa da aka gudanar don karrama Fayemi mai taken: “JKF: A Journey in Leadership”.

Bagudu ya ce, “Hatta manyan kasashe irinsu Amurka, wadanda sun fi Najeriya ci gaban tattalin arziki, sun ma fi Najeriya bashi. Abin da muke bukata yanzu shine saka hannun jari ta hanyar haɗin gwiwar duniya sama da mutane miliyan 200, don gina tattalin arzikinmu da gina jama’armu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp