Home DUNIYA Amurka na Dari-Darin Shiga Tattaunawar Shirin Nukiliyar Iran

Amurka na Dari-Darin Shiga Tattaunawar Shirin Nukiliyar Iran

Kasar Amurka tayi watsi da duk wani yunkuri na sake shiga tattaunawar farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran nan kusa, abinda ake gani zai dakushe fatan da ake da shi  na kulla sabuwar yarjejeniya akan wadda akayi a shekarar 2015.

Mai Magana da yawun fadar shugaban kasar John Kirby yace ba wai basa bukatar ganin an aiwatar da yarjejeniyar bace, sai dai a halin yanzu basu ga wata hanyar kulla ta ba a nan kusa.

Kirby yace abinda ke gabansu yanzu shine daukar mataki akan kasar Iran saboda yadda take murkushe masu zanga zangar adawa da mutuwar Mahsa Amini, matashiyar da aka samu da laifin kin sanya hijabi a ranar 16 ga watan Satumba.

Mai magana da yawun fadar shugaban yace har yanzu shugaba Joe Biden na nan kan matsayinsa cewar ba zai taba barin kasar Iran ta mallaki makamin nukiliya ba.

Zanga zanga ta barke a sassan kasar tun bayan mutuwar Amini, abinda ya kaiga arangama tsakanin Yan Sanda da masu adawa da matakin da jami’an tsaro suka dauka, abinda ya kaiga mutuwar mutane sama da 100 da kuma kama wasu sama da 100 da tuni aka gurfanar a gaban shari’a.

Shugaban Iran Ebrahim Raisi ya zargi Amurka da kawayenta da tinzira masu zanga zangar domin jefa kasar cikin tashin hankali, yayin da kasashen Turai suka amince da wani shirin kakabawa kasar takunkumi akan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp