Home DUNIYA Amurka na Dari-Darin Shiga Tattaunawar Shirin Nukiliyar Iran

Amurka na Dari-Darin Shiga Tattaunawar Shirin Nukiliyar Iran

Kasar Amurka tayi watsi da duk wani yunkuri na sake shiga tattaunawar farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran nan kusa, abinda ake gani zai dakushe fatan da ake da shi  na kulla sabuwar yarjejeniya akan wadda akayi a shekarar 2015.

Mai Magana da yawun fadar shugaban kasar John Kirby yace ba wai basa bukatar ganin an aiwatar da yarjejeniyar bace, sai dai a halin yanzu basu ga wata hanyar kulla ta ba a nan kusa.

Kirby yace abinda ke gabansu yanzu shine daukar mataki akan kasar Iran saboda yadda take murkushe masu zanga zangar adawa da mutuwar Mahsa Amini, matashiyar da aka samu da laifin kin sanya hijabi a ranar 16 ga watan Satumba.

Mai magana da yawun fadar shugaban yace har yanzu shugaba Joe Biden na nan kan matsayinsa cewar ba zai taba barin kasar Iran ta mallaki makamin nukiliya ba.

Zanga zanga ta barke a sassan kasar tun bayan mutuwar Amini, abinda ya kaiga arangama tsakanin Yan Sanda da masu adawa da matakin da jami’an tsaro suka dauka, abinda ya kaiga mutuwar mutane sama da 100 da kuma kama wasu sama da 100 da tuni aka gurfanar a gaban shari’a.

Shugaban Iran Ebrahim Raisi ya zargi Amurka da kawayenta da tinzira masu zanga zangar domin jefa kasar cikin tashin hankali, yayin da kasashen Turai suka amince da wani shirin kakabawa kasar takunkumi akan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp