Home General ASUU ta Janye Yajin Aiki da Take Tsawon Watannin 8

ASUU ta Janye Yajin Aiki da Take Tsawon Watannin 8

Kungiyar malaman Jami’oin Nijeriya ta (ASUU) ta dakatar da yajin aikin data kwashe tsawon watannin ta yi bisa wasu dalilai, kamar yadda kwamitin amintattun kungiyar ya shaidawa manema labarai a safiyar juma’a.

Kungiyar ta yanke hukuncin janye yajin aikin ne bayan wata ganawa da shuwagabannin suka fara gudanarwa tun daga daren alhamis zuwa wayewar garin juma’a.

Kungiyar ta kira taron gawanar ne domin yanke matakin ta na karshe bayan da mambobin ta na jihohi suka gana kan hukuncin kotun daukaka kara a makon daya gabata.

Kotun daukaka kara ta umarci kungiyar ASUU da ta dakatar da yajin aikin kafin a saurari daukaka karar da ta yanke, inda ta umarci malam su koma bakin aiki.

Mambobin kwamitin zartawa na kungiyar na kasa, wadanda suka hadar da shuwagabannin kungiyar na jihohin dana kasa ne suka halarci taron a sakatariyar kungiyar ta ASUU dake birnin tarayya Abuja.

Kungiyar malaman jami’oin ta ASUU ta tsunduma yajin aikin ne tun a 14 ga watan fabrerun 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp