Home DUNIYA Rundunar Sojin Benin ta dakile wani harin Ta’addanci a Arewacin kasar

Rundunar Sojin Benin ta dakile wani harin Ta’addanci a Arewacin kasar

Rundunar sojin Jamhuriyar Benin ta yi nasarar dakile wani hari da ‘yan ta’adda suka shirya kai wa yankin arewa maso yammacin kasar, wanda bayanai ke cewa ‘yan ta’addan sun kitsa yadda za a kai harin ne daga makwabtan kasar wato Jamhuriyar Nijar da Burkina Faso.

Sanarwar da rundunar sojin ta Benin ta fitar ta ce yayin dakatar da harin dakarun soji sun yi nasarar hallaka ‘yan ta‘adda 8, yayinda da dama suka tsere da munanan raunuka.

Wasu alkaluma na nuni da cewa rundunar Sojin ta Benin ta yi nasarar dakile hare-haren ta’addanci har sau 12 daga bara zuwa yanzu, dai dai lokacin da barazanar tsaro ke ci gaba da tsananta a kasashen yankin Sahel sakamakon yadda kungiyoyin ‘yan ta’adda masu alaka da Al Qaeda da kuma IS ke ci gaba da yawa bisa ikirarin aikata jihadi.

Sanarwar mai dauke da sa hannun jami’in yada Labarai na rundunar Sojin ta Benin, Ebnezer Honfonga ta ce da misalin karfe 12 na daren jiya ne sojojoji suka wargaza shirin ‘yan ta’adda na shiga kauyen Materi, da nufin kaddamar da jerin hare-hare.

Sai dai kuma bayan da rundunar Sojin ta samu bayanai sirri ne ta afka musu ta hanyar yi musu kwantan bauna, duk da dai sun yi yunkurin mayar da martani ta hanyar tashin bama bamai da harbe harbe.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp