Home DUNIYA Rundunar Sojin Benin ta dakile wani harin Ta’addanci a Arewacin kasar

Rundunar Sojin Benin ta dakile wani harin Ta’addanci a Arewacin kasar

Rundunar sojin Jamhuriyar Benin ta yi nasarar dakile wani hari da ‘yan ta’adda suka shirya kai wa yankin arewa maso yammacin kasar, wanda bayanai ke cewa ‘yan ta’addan sun kitsa yadda za a kai harin ne daga makwabtan kasar wato Jamhuriyar Nijar da Burkina Faso.

Sanarwar da rundunar sojin ta Benin ta fitar ta ce yayin dakatar da harin dakarun soji sun yi nasarar hallaka ‘yan ta‘adda 8, yayinda da dama suka tsere da munanan raunuka.

Wasu alkaluma na nuni da cewa rundunar Sojin ta Benin ta yi nasarar dakile hare-haren ta’addanci har sau 12 daga bara zuwa yanzu, dai dai lokacin da barazanar tsaro ke ci gaba da tsananta a kasashen yankin Sahel sakamakon yadda kungiyoyin ‘yan ta’adda masu alaka da Al Qaeda da kuma IS ke ci gaba da yawa bisa ikirarin aikata jihadi.

Sanarwar mai dauke da sa hannun jami’in yada Labarai na rundunar Sojin ta Benin, Ebnezer Honfonga ta ce da misalin karfe 12 na daren jiya ne sojojoji suka wargaza shirin ‘yan ta’adda na shiga kauyen Materi, da nufin kaddamar da jerin hare-hare.

Sai dai kuma bayan da rundunar Sojin ta samu bayanai sirri ne ta afka musu ta hanyar yi musu kwantan bauna, duk da dai sun yi yunkurin mayar da martani ta hanyar tashin bama bamai da harbe harbe.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp