Home DUNIYA Rundunar Sojin Benin ta dakile wani harin Ta’addanci a Arewacin kasar

Rundunar Sojin Benin ta dakile wani harin Ta’addanci a Arewacin kasar

Rundunar sojin Jamhuriyar Benin ta yi nasarar dakile wani hari da ‘yan ta’adda suka shirya kai wa yankin arewa maso yammacin kasar, wanda bayanai ke cewa ‘yan ta’addan sun kitsa yadda za a kai harin ne daga makwabtan kasar wato Jamhuriyar Nijar da Burkina Faso.

Sanarwar da rundunar sojin ta Benin ta fitar ta ce yayin dakatar da harin dakarun soji sun yi nasarar hallaka ‘yan ta‘adda 8, yayinda da dama suka tsere da munanan raunuka.

Wasu alkaluma na nuni da cewa rundunar Sojin ta Benin ta yi nasarar dakile hare-haren ta’addanci har sau 12 daga bara zuwa yanzu, dai dai lokacin da barazanar tsaro ke ci gaba da tsananta a kasashen yankin Sahel sakamakon yadda kungiyoyin ‘yan ta’adda masu alaka da Al Qaeda da kuma IS ke ci gaba da yawa bisa ikirarin aikata jihadi.

Sanarwar mai dauke da sa hannun jami’in yada Labarai na rundunar Sojin ta Benin, Ebnezer Honfonga ta ce da misalin karfe 12 na daren jiya ne sojojoji suka wargaza shirin ‘yan ta’adda na shiga kauyen Materi, da nufin kaddamar da jerin hare-hare.

Sai dai kuma bayan da rundunar Sojin ta samu bayanai sirri ne ta afka musu ta hanyar yi musu kwantan bauna, duk da dai sun yi yunkurin mayar da martani ta hanyar tashin bama bamai da harbe harbe.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp