Home Labarai Gwamnatin Jihar Zamfara ta Rufe wasu Yankuna a Jihar Saboda Tsaro

Gwamnatin Jihar Zamfara ta Rufe wasu Yankuna a Jihar Saboda Tsaro

Gwamnatin jihar Zamfara ta ce ta ɗauki matakin dakatar da kowace irin hada-hada a wasu yankunanta da ke fama da matsalar tsaro.

wannanna kunshe ne ta cikin wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar a ranar Juma’a, ta ce ta lura da yadda ake samun taɓarɓarewar tsaro ta hanyar sace-sacen al’umma a kauyuka da kuma kan wasu hanyoyin jihar.

A saboda haka sanarwar ta ce gwamnati ta kulle,  ƙananan hukumomin Anka da Bukuyum da kuma Gummi ɗungurungum.

Sauran kauyukan da kullewar ta shafa su ne Ƴarkofoji, da Birnin Tudu, da Rini, da Gora Namaye, da Janbako, da Faru, da Boko da kuma Mada.

Sanarwar ta kuma ce daga yau an rufe kasuwannin Danjibga da Bagega, Bugu da ƙari an dakatar da zirga-zirga kan hanyoyi da suka hadar da Colony zuwa Lambar Boko, Bakura zuwa Lambar Damri, Mayanchi zuwa Daki Takwas har zuwa Gummi, Daki Takwas zuwa Zuru, Kucheri zuwa Bawaganga zuwa Wanke, Magami zuwa Dangulbi sai kuma  Gusau zuwa Magami

Gwamnati ta ce an ɗauki matakin ne domin bai wa jami’an tsaro damar gudanar da ayyukansu ba tare da wani cikas ba.

Ta kuma ce ta bai wa jami’an tsaro umurnin ɗaukan mummunan mataki kan duk wanda aka samu da laifin karya dokar.

jihar Zamfara na  guda cikin jihohin  Arewa maso yammacin Nijeriya da matsalar tsaro kekara karama sakamakon  ƴanfashin daji da ta fi kassarar jihar dama yankin.

PRNigeria Haus

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp