Home DUNIYA Rasha za ta Gina Babbar Cibiyar Tara Gas a Turkiya don Maye...

Rasha za ta Gina Babbar Cibiyar Tara Gas a Turkiya don Maye Gurbin NordStream

Shugaba Recep Tayyip Erdogan na Turkiya ya goyi bayan shirin takwaransa na Rasha Vladimir Putin game da gina babbar cibiyar tara iskar gas a cikin kasar bayan da shugaban ya bayyana cewa wannan dabara ce da ke bukatar a aiwatar da ita a cikin gaggawa.

Jaridu a Ankara sun ruwaito cewa tun farko shugaba Vladimir Putin ne ya gabatarwa Erdogan shirin, a wani yunkuri na isar da makamashi kudancin Turai ta cikin Turkiya sakamakon matsalar da ake samu a aikin tura iskar gas din ta bututun gas din NordStream.

Tuni dai wannan mataki ya ja hankalin kasashen Turai musamman Faransa inda ofishin shugaba Emmanuel Macron ya fitar da sanarwar da ke sukar matakin wanda ya bayyana yunkurin na Rasha da Turkiya a matsayin abin da ya sabawa hankali.

Rasha wadda dama ita ke bai wa Turkiya makamashin gas ta hanyar bututun TurkStream da ke karkashin bakin teku wanda ya hada kasashen biyu, sabon yunkurin zai saukaka mata fitar da gas zuwa kasashen Turai wadanda ta ke jituwa da su tare zagaye wadanda ta ke takun saka da su.

Erdogan da ke sanar da wannan sabon yunkuri bayan dawowarsa daga ganawa da Putin a Kazakhstan jiya alhamis, ya ce ko shakka babu za a samar da rumbunan adana gas din a mahadar kasashen Turkiya da Bulgaria da kuma Girka.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp