Home DUNIYA Rasha za ta Gina Babbar Cibiyar Tara Gas a Turkiya don Maye...

Rasha za ta Gina Babbar Cibiyar Tara Gas a Turkiya don Maye Gurbin NordStream

Shugaba Recep Tayyip Erdogan na Turkiya ya goyi bayan shirin takwaransa na Rasha Vladimir Putin game da gina babbar cibiyar tara iskar gas a cikin kasar bayan da shugaban ya bayyana cewa wannan dabara ce da ke bukatar a aiwatar da ita a cikin gaggawa.

Jaridu a Ankara sun ruwaito cewa tun farko shugaba Vladimir Putin ne ya gabatarwa Erdogan shirin, a wani yunkuri na isar da makamashi kudancin Turai ta cikin Turkiya sakamakon matsalar da ake samu a aikin tura iskar gas din ta bututun gas din NordStream.

Tuni dai wannan mataki ya ja hankalin kasashen Turai musamman Faransa inda ofishin shugaba Emmanuel Macron ya fitar da sanarwar da ke sukar matakin wanda ya bayyana yunkurin na Rasha da Turkiya a matsayin abin da ya sabawa hankali.

Rasha wadda dama ita ke bai wa Turkiya makamashin gas ta hanyar bututun TurkStream da ke karkashin bakin teku wanda ya hada kasashen biyu, sabon yunkurin zai saukaka mata fitar da gas zuwa kasashen Turai wadanda ta ke jituwa da su tare zagaye wadanda ta ke takun saka da su.

Erdogan da ke sanar da wannan sabon yunkuri bayan dawowarsa daga ganawa da Putin a Kazakhstan jiya alhamis, ya ce ko shakka babu za a samar da rumbunan adana gas din a mahadar kasashen Turkiya da Bulgaria da kuma Girka.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp