Home Labarai Hukumar EFCC ta Kama Ma’aikatan Banki 12 da Zargin Satar kuɗaɗe

Hukumar EFCC ta Kama Ma’aikatan Banki 12 da Zargin Satar kuɗaɗe

Frauds

Hukumar EFCC ta Kama Ma’aikatan Banki 12 da Zargin Satar kuɗaɗe

 

Hukumar yaƙi da almundahana a Najeriya ta EFCC ta kama ma’aikatan banki 12 da zargin satar kuɗaɗe a wuraren aikinsu a Jihar Enugu da ke kudancin ƙasar.

A cewar hukumar, binciken farko-farko da ta gudanar ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun saci kuɗaɗe daga wasu asusu da ba sa aiki a wani daga cikin reshen bankunan da a yanzu ba sa aiki a jihar ta Enugu.

“An tura kuɗaɗen daga asusan da ke rufe zuwa ga mutane daban-daban, kuma tuni EFCC ta gano wanda ya fi kowa samun rabo mai tsoka,” a cewar sanarwar da hukumar ta fitar ranar Asabar.

Mutanen waɗanda suka ƙunshi mata huɗu da maza takwas, an kama su ne a ranar Juma’a kuma za su gurfana a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

An bayyana sunayensu da: Odeniyi Anthony, Deki Kingsley Onyekachi, Oguchukwu Ene, Elendu Chizaram, Anyakora Uchenna, Onah Kingsley, Akwe Elizabeth and Chinenye Grace Acibe, Victoria Ezedie, Chidi-Ukah Obinna, Etoh Lawrence Uzochukwu, Udeze Harrison

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp