Home DUNIYA Ana Zanga-Zanga kan Tabarbarewar Tattalin Arziki A Tunisia

Ana Zanga-Zanga kan Tabarbarewar Tattalin Arziki A Tunisia

Dubu Dubatar ‘yan kasar Tunisiya ne suka gudanar da zanga-zanga a birnin Tunis a jiya asabar don yin tir da manufofin shugaba Kais Sa’id, wanda suke zargin shi ne ke da alhakin tabarbarewar tattalin arzikin kasar, wanda ke fuskantar matsalar karancin kayan masarufi da hauhawar farashin kayayyaki.

A karkashin jagorancin jam’iyyar National Salvation Front, gamayyar jam’iyyun adawa masu zanga-zangar sun tsallaka manyan titunan babban birnin Tunisiya, suna kira da shugaban ya yi murabus.

Wannan zanga-zangar tana nuna fushin halin da ake ciki a Tunisiya karkashin Kais Saied da kuma kira da  ya yi murabus, kamar yada tsohon Fira Minista Ali Laaraydh, mataimakin shugaban Ennahdha, ya shaida wa manema labarai.

A dai-dai lokacin da jama’a ke gudanar da wannan zanga-zanga ,asusun ba da lamuni na duniya IMF ya cimma yarjejeniya da gwamnatin kasar ta Tunisia wadda za ta bada damar biyan dala biliyan 1.9 yayin da Tunisia ke fama da matsananciyar matsalar tattalin arziki.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp