Home DUNIYA Ana Zanga-Zanga kan Tabarbarewar Tattalin Arziki A Tunisia

Ana Zanga-Zanga kan Tabarbarewar Tattalin Arziki A Tunisia

Dubu Dubatar ‘yan kasar Tunisiya ne suka gudanar da zanga-zanga a birnin Tunis a jiya asabar don yin tir da manufofin shugaba Kais Sa’id, wanda suke zargin shi ne ke da alhakin tabarbarewar tattalin arzikin kasar, wanda ke fuskantar matsalar karancin kayan masarufi da hauhawar farashin kayayyaki.

A karkashin jagorancin jam’iyyar National Salvation Front, gamayyar jam’iyyun adawa masu zanga-zangar sun tsallaka manyan titunan babban birnin Tunisiya, suna kira da shugaban ya yi murabus.

Wannan zanga-zangar tana nuna fushin halin da ake ciki a Tunisiya karkashin Kais Saied da kuma kira da  ya yi murabus, kamar yada tsohon Fira Minista Ali Laaraydh, mataimakin shugaban Ennahdha, ya shaida wa manema labarai.

A dai-dai lokacin da jama’a ke gudanar da wannan zanga-zanga ,asusun ba da lamuni na duniya IMF ya cimma yarjejeniya da gwamnatin kasar ta Tunisia wadda za ta bada damar biyan dala biliyan 1.9 yayin da Tunisia ke fama da matsananciyar matsalar tattalin arziki.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp