Home Labarai Hukumar EFCC ta Kama Ma’aikatan Banki 12 da Zargin Satar kuɗaɗe

Hukumar EFCC ta Kama Ma’aikatan Banki 12 da Zargin Satar kuɗaɗe

Frauds

Hukumar EFCC ta Kama Ma’aikatan Banki 12 da Zargin Satar kuɗaɗe

 

Hukumar yaƙi da almundahana a Najeriya ta EFCC ta kama ma’aikatan banki 12 da zargin satar kuɗaɗe a wuraren aikinsu a Jihar Enugu da ke kudancin ƙasar.

A cewar hukumar, binciken farko-farko da ta gudanar ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun saci kuɗaɗe daga wasu asusu da ba sa aiki a wani daga cikin reshen bankunan da a yanzu ba sa aiki a jihar ta Enugu.

“An tura kuɗaɗen daga asusan da ke rufe zuwa ga mutane daban-daban, kuma tuni EFCC ta gano wanda ya fi kowa samun rabo mai tsoka,” a cewar sanarwar da hukumar ta fitar ranar Asabar.

Mutanen waɗanda suka ƙunshi mata huɗu da maza takwas, an kama su ne a ranar Juma’a kuma za su gurfana a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

An bayyana sunayensu da: Odeniyi Anthony, Deki Kingsley Onyekachi, Oguchukwu Ene, Elendu Chizaram, Anyakora Uchenna, Onah Kingsley, Akwe Elizabeth and Chinenye Grace Acibe, Victoria Ezedie, Chidi-Ukah Obinna, Etoh Lawrence Uzochukwu, Udeze Harrison

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp