Home Labarai Hukumar EFCC ta Kama Ma’aikatan Banki 12 da Zargin Satar kuɗaɗe

Hukumar EFCC ta Kama Ma’aikatan Banki 12 da Zargin Satar kuɗaɗe

Frauds

Hukumar EFCC ta Kama Ma’aikatan Banki 12 da Zargin Satar kuɗaɗe

 

Hukumar yaƙi da almundahana a Najeriya ta EFCC ta kama ma’aikatan banki 12 da zargin satar kuɗaɗe a wuraren aikinsu a Jihar Enugu da ke kudancin ƙasar.

A cewar hukumar, binciken farko-farko da ta gudanar ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun saci kuɗaɗe daga wasu asusu da ba sa aiki a wani daga cikin reshen bankunan da a yanzu ba sa aiki a jihar ta Enugu.

“An tura kuɗaɗen daga asusan da ke rufe zuwa ga mutane daban-daban, kuma tuni EFCC ta gano wanda ya fi kowa samun rabo mai tsoka,” a cewar sanarwar da hukumar ta fitar ranar Asabar.

Mutanen waɗanda suka ƙunshi mata huɗu da maza takwas, an kama su ne a ranar Juma’a kuma za su gurfana a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

An bayyana sunayensu da: Odeniyi Anthony, Deki Kingsley Onyekachi, Oguchukwu Ene, Elendu Chizaram, Anyakora Uchenna, Onah Kingsley, Akwe Elizabeth and Chinenye Grace Acibe, Victoria Ezedie, Chidi-Ukah Obinna, Etoh Lawrence Uzochukwu, Udeze Harrison

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp