Home DUNIYA Sarki Charles na III ya tabbatar da Rishi Sunak Matsayin Firaministan Birtaniya

Sarki Charles na III ya tabbatar da Rishi Sunak Matsayin Firaministan Birtaniya

Sarki Charles na III ya  tabbatar da Rishi Sunak matsayin Firaministan Birtaniya, kuma bayan tabbatarwar ya sha alwashin gyara kurakuran da aka tafka wadanda suka kai kasar ga fadawa halin matsananciyar matsalar tattalin arziki.

Sunak mabiyin addinin Hindu mai shekaru 42 wanda Sarki Charles na 3 ya tabbatar da shi a matsayin Firaminista da misalin karfe 11 da mintuna 15 na safiyar yau talata, shi ne Firaminista na 3 da kasar ta gani cikin shekarar nan.

Wannan ne dai nadi na farko da Sarki Charles na 3 ya jagoranta la’akari da cewa Sarauniya Elizabeth ce ta tabbatar da nadin Liz Truss kwanaki kalilan gabanin mutuwarta.

Jim kadan bayan tabbatar da shi, Rishi Sunak ya ce aiki na farko da zai sanya a gaba shi ne samar da sauye-sauye don gyara ga kura-kuren da aka tafka cikin makwanni 7 na mulkinta Truss lamarin da ya durkusar da tattalin arziki.

A cewarsa baya zargin Truss kuma matakan da ta dauka ba gazawa ba ce, haka zalika bada mummunar manufa ta samar da sauye-sauyen da suka illa ga tattalin arziki ba, hasalima tsari ne mai kyau sai dai sun juye zuwa matsala ne saboda halin da Duniya ke ciki.

Yayin jawabinta na ban kwana Truss ta yiwa Sunak fatan alkhairi da kuma fatar warwarewar matsalolin da suka dabaibaye sashen tattalin arzikin kasar wanda ya jefa jama’a a halin matsin tattalin arziki.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp