Home DUNIYA Buhari: Nijeriya na fatan yin Aiki da Burtaniya

Buhari: Nijeriya na fatan yin Aiki da Burtaniya

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa Nijeriya na fatan yin aiki tare da sabon firaministan Burtaniya Rishi Sunak, a banagarori da dama da suka hadar da yaki da ta’addanci, samar da abinci gami da makamashi da tunkarara matsalar sauyin yanayi.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata takardar sanarwa da kakakin shugaban kasa Garba shehu ya fitar, mai taken kalaman shugaba muhammadu Buhari kan firamininsta burtaniya mai jiran gado, Rt Hon. Rishi Sunak MP.

Sanarwar take madadin gwamnatin tarayyar Nijeriya, dake matsayin babbar kasa cikin kasashe 21 na Nahiyar Afirka dake kkungiyar kasashe rainon Ingila ta commonwealth na yiwa Rishi Sunak maraba da shiga Ofishi.

“Matsayinsa na firaminista na farko daga jini biyu wato burtaniya da Asiya kuma mafi kankata a cikin shekaru 200, wannan zai kasance wani abin laka’akai ga matasa a cikin al’ummar mu biliyan 2.4 a kasashe 56 na Commonwealth”.

“A wannan muhimmayar rana, yana da kyau mu tuna da kyakkyawar alakar dake tsakanin kasashen mu Burtaniya da Nijeriya”.

Shugaban ya kara da cewa kungiyar kasashe renon ingila za ta tsaya tsayin daka wajen yakar ta’addanci tare da sabunta kudirorin ta na magance matsalar karancin abinci a duniya da ke haddasa tsadar rayuwa ga Al’ummomin duniya baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp