Home DUNIYA Buhari: Nijeriya na fatan yin Aiki da Burtaniya

Buhari: Nijeriya na fatan yin Aiki da Burtaniya

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa Nijeriya na fatan yin aiki tare da sabon firaministan Burtaniya Rishi Sunak, a banagarori da dama da suka hadar da yaki da ta’addanci, samar da abinci gami da makamashi da tunkarara matsalar sauyin yanayi.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata takardar sanarwa da kakakin shugaban kasa Garba shehu ya fitar, mai taken kalaman shugaba muhammadu Buhari kan firamininsta burtaniya mai jiran gado, Rt Hon. Rishi Sunak MP.

Sanarwar take madadin gwamnatin tarayyar Nijeriya, dake matsayin babbar kasa cikin kasashe 21 na Nahiyar Afirka dake kkungiyar kasashe rainon Ingila ta commonwealth na yiwa Rishi Sunak maraba da shiga Ofishi.

“Matsayinsa na firaminista na farko daga jini biyu wato burtaniya da Asiya kuma mafi kankata a cikin shekaru 200, wannan zai kasance wani abin laka’akai ga matasa a cikin al’ummar mu biliyan 2.4 a kasashe 56 na Commonwealth”.

“A wannan muhimmayar rana, yana da kyau mu tuna da kyakkyawar alakar dake tsakanin kasashen mu Burtaniya da Nijeriya”.

Shugaban ya kara da cewa kungiyar kasashe renon ingila za ta tsaya tsayin daka wajen yakar ta’addanci tare da sabunta kudirorin ta na magance matsalar karancin abinci a duniya da ke haddasa tsadar rayuwa ga Al’ummomin duniya baki daya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp