Home Labarai Iyalai sun Koka yayin da Masu Garkuwa da Mutane ke Neman Kudin...

Iyalai sun Koka yayin da Masu Garkuwa da Mutane ke Neman Kudin Fansa N550m ga Fasinjojin da aka Sace

Iyalai sun Koka yayin da Masu Garkuwa da Mutane ke Neman Kudin Fansa N550m ga Fasinjojin da aka Sace

 

Wasu ‘yan bindiga da suka yi garkuwa da fasinjoji 11 a ranar Juma’a a kan iyakar Nasarawa da Benuwai sun bukaci a biya su Naira miliyan 50 ga kowane daya daga cikin wadanda abin ya shafa.

A baya an ruwaito cewa fasinjojin sun shiga wata motar safa ne a garin Jos na jihar Filato, inda suka nufi Onitsha na jihar Anambra, inda aka kai musu hari.

A halin da ake ciki dai, masu garkuwa da mutanen sun fara tuntubar kamfanin sufuri inda suka bukaci a biya su Naira miliyan 50 ga kowane fasinjojin da aka sace.

An ce daga baya ‘yan bindigar sun kira iyalan wadanda abin ya shafa domin neman kudin.

Wasu daga cikin iyalan sun shaida wa wakilinmu cewa, suna kokawa wajen samun kudaden ne bayan tattaunawa da masu garkuwa da mutane.

Wani magidanci da mahaifiyarsa na cikin wadanda lamarin ya shafa kuma ya nemi a sakaya sunansa saboda tsaro, ya ce rayuwa babu ita da wahala.

Ya ce, “Mahaifiyata ta je binne su ne aka kai musu hari aka yi garkuwa da su. Hatta motar da ke dauke da gawar da suke kai gida tana gaban motar su ne lamarin ya faru. Bayan motar daukar marasa lafiya ta wuce inda ‘yan bindigar ke buya, sai motar bas da ke dauke da mahaifiyata da sauran fasinjojin masu garkuwa da mutane suka tare su.”

Wani uba wanda shi ma ya nemi a sakaya sunansa, ya ce dansa na komawa makaranta lokacin da aka yi garkuwa da shi.

“Ba shi da lafiya lokacin da ASUU ta janye yajin aikin. Ya ce min zai iya komawa makaranta don ya san halin da ake ciki a makarantar. Satar da aka yi ya yi mana rauni,” ya kara da cewa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Filato, DSP Alabo Alfred, ya mika wa wakilinmu ga rundunar ‘yan sandan jihar Benuwe, inda ya ce lamarin bai faru a yankinsa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp