Hukumar NDLEA ta Kama Masu Safarar Koken daga Kasashen Ketare zuwa Kasar

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya NDLEA ta ce jami’anta sun kama wani ɗan Nijar da ‘yan Pakistan biyu bisa zargin safarar koken.

A sakon da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita ta ce an kama ‘yan Pakistan din a filin jirgin sama na Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya, yayin da aka kama ɗan Nijar ɗin a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin ƙasar

Hukumar ta ce ta kama ‘yan Pakistan ɗin – masu suna Asif Muhammed mai shekara 45, da kuma Hussain Naveed, mai shekara 57 – da laifin safarar koken da nauyinta ya kai kilo 2,985.5kg, a yayin da suke shirin hawa jirgi zuwa birnin Lahore na Pakistan.

Sanarwar ta ci gaba da cewa mutanen na da takardun izinin zama a Najeriya, waɗanda take zargin cewa na bogi ne, kuma suna yawan zuwa Najeriya da nufin yin kasuwancin atamfofi.

Emergency Digest

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 31 minutes 44 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 13 minutes 9 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com