Home Labarai Shugabannin Kungiyar ASUU na Ganawar Gaggawa

Shugabannin Kungiyar ASUU na Ganawar Gaggawa

Shugabannin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya ASUU sun shiga ganawar sirri ta gaggawa.

An ruwaito cewa kungiyar ta shiga ganawar sirrin ne da tsakar ranar Litinin, a harabar sakatariyar kungiyar da ke jami’ar Abuja.

Ganawar karkashin jagorancin shugaban kungiyar Farfesa Emmanuel Osodeke, za ta duba batun biyan malaman rabin albashin watan Oktoba.

Tun da fari dai kungiyar reshen jami’ar Jos Sun dakatar da mambobin su da zuwa aiki har sai gwamnatin tarayya ta biya su cikakken Albashin su, duk da sun bayyana cewa ba yajin aiki suka shiga ba.

Sai dai daga bisani gwamantin Nijeriya ta Magantu kan  biyan su ALbashin na kwanaki 17 da suka yi aiki a cikin su, duk da abinda kungiyar ta kira alkawarin gwamantin tarayya ta dauka musu na biyan su Albashin watan na Oktoba cikakken.

Idan dai za’a iya tunawa kugiyar malaman Jami’oin Nijeriya ta tsunduma yajin aiki ne bisa abinda ta kira gazawar gwamnatin kasar na gaza biya mata bukatun da ta nema, yajin aikin da suka kwashe watanni 8 ba tare da sun shiga ajujuwan sub a domin koyar da dalibai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp