Shugabannin Kungiyar ASUU na Ganawar Gaggawa

Shugabannin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya ASUU sun shiga ganawar sirri ta gaggawa.

An ruwaito cewa kungiyar ta shiga ganawar sirrin ne da tsakar ranar Litinin, a harabar sakatariyar kungiyar da ke jami’ar Abuja.

Ganawar karkashin jagorancin shugaban kungiyar Farfesa Emmanuel Osodeke, za ta duba batun biyan malaman rabin albashin watan Oktoba.

Tun da fari dai kungiyar reshen jami’ar Jos Sun dakatar da mambobin su da zuwa aiki har sai gwamnatin tarayya ta biya su cikakken Albashin su, duk da sun bayyana cewa ba yajin aiki suka shiga ba.

Sai dai daga bisani gwamantin Nijeriya ta Magantu kan  biyan su ALbashin na kwanaki 17 da suka yi aiki a cikin su, duk da abinda kungiyar ta kira alkawarin gwamantin tarayya ta dauka musu na biyan su Albashin watan na Oktoba cikakken.

Idan dai za’a iya tunawa kugiyar malaman Jami’oin Nijeriya ta tsunduma yajin aiki ne bisa abinda ta kira gazawar gwamnatin kasar na gaza biya mata bukatun da ta nema, yajin aikin da suka kwashe watanni 8 ba tare da sun shiga ajujuwan sub a domin koyar da dalibai.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 34 minutes 38 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 16 minutes 3 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com