Home Labarai EFCC ta Cafke Mustapha Naira Mai Canjin Kudi a Abuja

EFCC ta Cafke Mustapha Naira Mai Canjin Kudi a Abuja

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ta EFCC ta cafke wani mutum mai suna Mustapha Muhammad, wanda aka fi sani da  Mustapha Naira bisa zargin yada jita-jita a fannin harkokin kudi a kasar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da hukumar ta ranar talata, wanda hukumar ta bayyana cewa ta kama shi ne ranar 12 ga watan nuwamba a yankin wuse zone B wadda ke matsayin cibiyar hada-hadar kasuwancin chanjin kudi a birnin tarayya Abuja.

Hukumar tace kame na guda cikin ayyukan da ta ke yin a tsaftace harkokin chanjin kudaden waje da kuma kawar da dukka masu kawo tasgaro a fannin da kuma yin zagon kasa ga tattalin arzikin kasar.

“wanda ake zargin yayi wasu bayanai masu amfani a daidai lokacin da ake tsaka da gudanar da bincike” a cewar EFCC.

Idan dai za’a iya tunawa hukumar EFCC ta kai sumame kasuwannin chanjin kudi, dake Nijeriya da suka hadar da jihohin legas, kano dama birnin tarayya kasar Abuja, wani bangare na dakatar da sauyin kudin kasar da Dalar Amurka abinda ake kallon ya kara sanya farashin dalar tashin gwauron zabi.

An zargi yadda wasu ke halasta kudin haram ta hanyar sauya su da dala, da nufin kada su yi asarar su sakamakon sake fasalin kudin kasar da Gwamnati tayi Shirin yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp