Home Labarai INEC za ta Tattauna da Ganduje, Bala Muhammad, da Jami’an Tsaro Kan...

INEC za ta Tattauna da Ganduje, Bala Muhammad, da Jami’an Tsaro Kan Batutuwan Zaben 2023

Hukumar zabe mai zaman kanta za ta tattauna da jiga-jigan siyasar kasar nan kan batutuwan da suka shafi zaben 2023.

An gayyaci wasu gwamnoni, dan takarar shugaban kasa da sauran masu ruwa da tsaki na kasar nan.

Majiya ta bayyana maudu’in da za a tattauna a kai don shawo kalubalen tsaro a zaben 2023 mai zuwa na badi.

FCT, Abuja – Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) a ranar Talata mai zuwa za ta gana da gwamnoni, jami’an tsaro da dan takarar shugaban kasa gabanin zaben 2023 mai zuwa nan kusa.

Za a yi tattaunawar ne a Nicon Luxury a birnin tarayya Abuja tare da kwamishinan INEC kan harkokin wayar da masu kada kuri’u, Festu Okoye, Punch ta ruwaito.

A bangaren ‘yan siyasa, za a zauna da gwamna Abdullahi Ganduje na Kano, gwamna Bala Muhammad na Bauchi da gwamna Samuel Ortom na jhar Benue.

A bangaren hukumomin tsaro, za a yi zaman tare da sufeta janar na ‘yan sanda, Usman Alkali Baba da dai sauransu.

Hakazalika, za a yi da dan takarar shugaban kas ana jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, shugaban majalisar zauren shawarin jam’iyyun siyasa, Yabagi Sani, kungiyar ‘yan jarida da sauran masu ruwa da tsaki a harkar zabe.

Wannan batu dai na fitowa ne a cikin wata sanarwa da wanda ya shirya zaman, Edwin Olofu ya fitar a ranar Laraba 16 ga watan Nuwamba.

Olofu, wanda kuma shine manajan daraktan jarida Platinum Post ya bayyana cewa, wadanda za su halarci zaman za su tafka muhawara ne kan yadda za a yi zabe cikin lumana a badi.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, Hamza Al-Mustapha zai yi fashin baki kan maudu’i matsalolin na zamani da kalubalensu da kuma illar hakan ga zaben 2023.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp