Home Labarai Bincike: Kashi 65% Na Talakawan Nijeriya na Zaune ne a Arewancin Kasar

Bincike: Kashi 65% Na Talakawan Nijeriya na Zaune ne a Arewancin Kasar

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta bayyana cewa kashi 63 cikin 100 na mutanen Najeriya kusan miliyan 133 na fama da komajin talauci.

An gabatar da wannan adadi ne yayin kaddamar da bincike kan Talauci na Najeriya na Multidimensional Poverty Index (MPI) a birnin Abuja ranar Alhamis.

PRNigeria ta ruwaito cewa, ma’aunin da aka yi amfani da shi wajen kididdige wannan adadi ya samo asali ne a kan Multidimensional Poverty Index (MPI) Inda Akai la’akari da bangarori biyar cikin wadanda suka hadar da kiwon lafiya, yadda ake rayuwa, da ilimi, gami da tsaro da kuma rashin aikin yi.

Binciken wanda aka yi samfuri da gidaje sama da 56,000 a fadin Jihohi 36 na kasar gami da Babban Birnin Tarayya Abuja, wanda aka gudanar tsakanin watan Nuwamba 2021 zuwa Fabrairu 2022, ya nuna cewa kashi 65 cikin 100 na talakawan kasar, miliyan 86, suna zaune ne a Arewa, yayin da kashi 35, kusan Miliyan 47 suna zaune a Kudu.

Binciken ya bayyana jihar Sokoto a matsayin jihar da  tafi kowacce jiha yawan masu fama da talauci a fadin ƙasar,  inda take da kashi 91 cikin dari yayin da Ondo ke da kaso 27 cikin dari.

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya ce an dauki matakin ne don gano adadin masu fama da talauci da kuma hanyoyin da Za’a fito da manufofi Masu kyau don kawar da talaucin a cikin al’umma.

Buhari wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar sa Farfesa Ibrahim Gambari.

Rahoton ya kara da cewa, “sama da rabin al’ummar Najeriya talakawa ne da suke amfani da kawayi ko ita ce wajen yin girki maimakon makamashi mai tsafta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp