Home Labarai Bincike: Kashi 65% Na Talakawan Nijeriya na Zaune ne a Arewancin Kasar

Bincike: Kashi 65% Na Talakawan Nijeriya na Zaune ne a Arewancin Kasar

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta bayyana cewa kashi 63 cikin 100 na mutanen Najeriya kusan miliyan 133 na fama da komajin talauci.

An gabatar da wannan adadi ne yayin kaddamar da bincike kan Talauci na Najeriya na Multidimensional Poverty Index (MPI) a birnin Abuja ranar Alhamis.

PRNigeria ta ruwaito cewa, ma’aunin da aka yi amfani da shi wajen kididdige wannan adadi ya samo asali ne a kan Multidimensional Poverty Index (MPI) Inda Akai la’akari da bangarori biyar cikin wadanda suka hadar da kiwon lafiya, yadda ake rayuwa, da ilimi, gami da tsaro da kuma rashin aikin yi.

Binciken wanda aka yi samfuri da gidaje sama da 56,000 a fadin Jihohi 36 na kasar gami da Babban Birnin Tarayya Abuja, wanda aka gudanar tsakanin watan Nuwamba 2021 zuwa Fabrairu 2022, ya nuna cewa kashi 65 cikin 100 na talakawan kasar, miliyan 86, suna zaune ne a Arewa, yayin da kashi 35, kusan Miliyan 47 suna zaune a Kudu.

Binciken ya bayyana jihar Sokoto a matsayin jihar da  tafi kowacce jiha yawan masu fama da talauci a fadin ƙasar,  inda take da kashi 91 cikin dari yayin da Ondo ke da kaso 27 cikin dari.

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya ce an dauki matakin ne don gano adadin masu fama da talauci da kuma hanyoyin da Za’a fito da manufofi Masu kyau don kawar da talaucin a cikin al’umma.

Buhari wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar sa Farfesa Ibrahim Gambari.

Rahoton ya kara da cewa, “sama da rabin al’ummar Najeriya talakawa ne da suke amfani da kawayi ko ita ce wajen yin girki maimakon makamashi mai tsafta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp