Home Labarai Bincike: Kashi 65% Na Talakawan Nijeriya na Zaune ne a Arewancin Kasar

Bincike: Kashi 65% Na Talakawan Nijeriya na Zaune ne a Arewancin Kasar

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta bayyana cewa kashi 63 cikin 100 na mutanen Najeriya kusan miliyan 133 na fama da komajin talauci.

An gabatar da wannan adadi ne yayin kaddamar da bincike kan Talauci na Najeriya na Multidimensional Poverty Index (MPI) a birnin Abuja ranar Alhamis.

PRNigeria ta ruwaito cewa, ma’aunin da aka yi amfani da shi wajen kididdige wannan adadi ya samo asali ne a kan Multidimensional Poverty Index (MPI) Inda Akai la’akari da bangarori biyar cikin wadanda suka hadar da kiwon lafiya, yadda ake rayuwa, da ilimi, gami da tsaro da kuma rashin aikin yi.

Binciken wanda aka yi samfuri da gidaje sama da 56,000 a fadin Jihohi 36 na kasar gami da Babban Birnin Tarayya Abuja, wanda aka gudanar tsakanin watan Nuwamba 2021 zuwa Fabrairu 2022, ya nuna cewa kashi 65 cikin 100 na talakawan kasar, miliyan 86, suna zaune ne a Arewa, yayin da kashi 35, kusan Miliyan 47 suna zaune a Kudu.

Binciken ya bayyana jihar Sokoto a matsayin jihar da  tafi kowacce jiha yawan masu fama da talauci a fadin ƙasar,  inda take da kashi 91 cikin dari yayin da Ondo ke da kaso 27 cikin dari.

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya ce an dauki matakin ne don gano adadin masu fama da talauci da kuma hanyoyin da Za’a fito da manufofi Masu kyau don kawar da talaucin a cikin al’umma.

Buhari wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar sa Farfesa Ibrahim Gambari.

Rahoton ya kara da cewa, “sama da rabin al’ummar Najeriya talakawa ne da suke amfani da kawayi ko ita ce wajen yin girki maimakon makamashi mai tsafta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp