Mahukunta a Najeriya sun ce daga yanzu matafiya sun dai na nuna sakamakon basa dauke da cutar korona idan sun isa ko kuma za su yi tafiya zuwa wata kasa.
Read Also:
Hukumar kula da zirga zirgar jiragen sama ta kasar ta ce an dauki matakin hakan ne bayan tabbatar da cewa a yanzu ba kasafai ake samun wadanda suka kamu da cutar ba a kasar dama sauran kasashen duniya.
Hukumar ta ce daga yanzu duk wani matafiyi daga gida Najeriya da ma wadanda suka dawo daga wata kasar ba za a bukaci sakamakon gwajin cutar da ya nuna basa dauke da ita ba.
A baya dai wajibi ne ga duk matafiya suyi gwajin cutar kafin tafiya, haka ma wadanda suka dawo dole su nuna sakamakon gwajin da ya nuna basa dauke da ita.