Home General Ganduje: A shirye Nake na Saka hannu kan Hukuncin Abduljabbar

Ganduje: A shirye Nake na Saka hannu kan Hukuncin Abduljabbar

Gwamnatin jihar Kano ta ce gwamna Abdullahi Umar Ganduje a shirye ya ke ya sanya hannu kan sammacin kashe malamin Abduljabbar Nasiru Kabara.

Kwamishinan shari’a kuma babban lauyan jihar, Lawan Musa ne ya bayyana hakan a yayin da yake mayar da martani kan hukuncin da aka yankewa Abduljabbar na hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan da wata kotun shari’ar musulunci ta same shi da laifin yin kalaman batanci ga Annabi S.A.W.

Musa ya ce gwamnan a shirye yake domin ganin ba a karya doka da oda a jihar kano ba, inda ya ce hukuncin da kotun ta yanke akan malamin gwamnatin jihar ta shigar da karar malamin, wanda hakan ke nuna babu wanda ya fi karfin doka.

Ba za a bar kowa ya karya doka ba tare da daukar matakan da suka dace akansa ba.

“Mun kai shi (Abduljabbar) kotu, muka ba shi dukkan abubuwan da ya kamata domin ya kare kansa, kuma a yau mun gode wa Allah, kotu ta gamsu da hujjojin da muka gabatar a kansa, kuma ta yanke masa hukuncin da ya dace,” inji shi.

Ya kara da cewa: “Kamar yadda gwamna bai canza matsayarsa ba a al’amarin Hanifa, haka nan ma ba ta canza ba akan wannan lamari.

“Kun san akwai tsare-tsare da yawa da ya kamata a bi kuma mai girma Gwamna a shirye yake; da zarar an kawo masa wannan takardar, zai sa hannu domin zartar da hukuncin”. a cewar kwamishinan

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp