Home General Hukumar DSS ta bukaci Al’ummar Nijeriya su gudanar da Shagulgulan Karshen shekara...

Hukumar DSS ta bukaci Al’ummar Nijeriya su gudanar da Shagulgulan Karshen shekara cikin lumana

Gabatowar bukuKuwan Kirsimeti da karshen shekara hukumar tsaro ta farin kaya a Nijeriya, ta bukaci Al’ummar kasar da su gudanar da bukukuwan cikin kwanciyar hankali da bin doka da Oda.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar na kasa Peter Afunanya, Ph.D, fsi Ya sanyawa hannu, mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Disambar 2022, aka raba ga manema labarai a birnin Abuja.
Hukumar tace zata hada hannu da dukkan masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da doka da Oda, don haka tana kira ga Al’umma, Malamai da ‘yan siyasa, shuwagabanni da Suyi wa’azuzzuka ko jawabai Da zasu tabbatar da zaman lafiya, samar da hadin kai, gami da wayar da kan mabiyan su hanyoyin da zasu kare kansu a yayin bukukuwan.
Wannan shi yafi dacewa kasancewar kada wasu suyi amfani da damar wajen tada zaune tsaye.
Hakazalika ‘yan siyasa a yayin da suke yakin neman zabe, ana so su gudanar cikin ka’ida, ya kamata su nisan ci labaran karya, kalaman kyama, tashin hankali da dukkan Abubuwan da zasu kassara tsaron kasa.
Haka kuma sanarwar ta bukaci ‘yan kasuwa dasu gujewa dabi’un da zasu haifar da hauhawar farashin maras fa’ida, kagar karancin samfuran kayayyaki abun da ka iya haifar da tashin hankali ta hanyar jifa Al’umma cikin halin rashin tabbas.
Hukumar ta kuma bukaci ‘yan Jarida da kungiyoyi masu zaman kansu da su kasance masu kishin kasa a yayin gudanar da ayyukan su matsayin su na masu ruwa da tsaki a fannin gina kasa da godabar da harkokin tsaron ta.
Daga Bisani shugaban Hukumar Alhaji Y. M Bichi, CFR, fwc a madadin jami’an hukumar yana Fatan Al’ummar zasu gudanar da bikin cikin kwanciyar hankali tare da tayasu murnar sabuwar shekara
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp