Home General Hukumar DSS ta bukaci Al’ummar Nijeriya su gudanar da Shagulgulan Karshen shekara...

Hukumar DSS ta bukaci Al’ummar Nijeriya su gudanar da Shagulgulan Karshen shekara cikin lumana

Gabatowar bukuKuwan Kirsimeti da karshen shekara hukumar tsaro ta farin kaya a Nijeriya, ta bukaci Al’ummar kasar da su gudanar da bukukuwan cikin kwanciyar hankali da bin doka da Oda.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar na kasa Peter Afunanya, Ph.D, fsi Ya sanyawa hannu, mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Disambar 2022, aka raba ga manema labarai a birnin Abuja.
Hukumar tace zata hada hannu da dukkan masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da doka da Oda, don haka tana kira ga Al’umma, Malamai da ‘yan siyasa, shuwagabanni da Suyi wa’azuzzuka ko jawabai Da zasu tabbatar da zaman lafiya, samar da hadin kai, gami da wayar da kan mabiyan su hanyoyin da zasu kare kansu a yayin bukukuwan.
Wannan shi yafi dacewa kasancewar kada wasu suyi amfani da damar wajen tada zaune tsaye.
Hakazalika ‘yan siyasa a yayin da suke yakin neman zabe, ana so su gudanar cikin ka’ida, ya kamata su nisan ci labaran karya, kalaman kyama, tashin hankali da dukkan Abubuwan da zasu kassara tsaron kasa.
Haka kuma sanarwar ta bukaci ‘yan kasuwa dasu gujewa dabi’un da zasu haifar da hauhawar farashin maras fa’ida, kagar karancin samfuran kayayyaki abun da ka iya haifar da tashin hankali ta hanyar jifa Al’umma cikin halin rashin tabbas.
Hukumar ta kuma bukaci ‘yan Jarida da kungiyoyi masu zaman kansu da su kasance masu kishin kasa a yayin gudanar da ayyukan su matsayin su na masu ruwa da tsaki a fannin gina kasa da godabar da harkokin tsaron ta.
Daga Bisani shugaban Hukumar Alhaji Y. M Bichi, CFR, fwc a madadin jami’an hukumar yana Fatan Al’ummar zasu gudanar da bikin cikin kwanciyar hankali tare da tayasu murnar sabuwar shekara
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp