Home General Hukumar DSS ta bukaci Al’ummar Nijeriya su gudanar da Shagulgulan Karshen shekara...

Hukumar DSS ta bukaci Al’ummar Nijeriya su gudanar da Shagulgulan Karshen shekara cikin lumana

Gabatowar bukuKuwan Kirsimeti da karshen shekara hukumar tsaro ta farin kaya a Nijeriya, ta bukaci Al’ummar kasar da su gudanar da bukukuwan cikin kwanciyar hankali da bin doka da Oda.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar na kasa Peter Afunanya, Ph.D, fsi Ya sanyawa hannu, mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Disambar 2022, aka raba ga manema labarai a birnin Abuja.
Hukumar tace zata hada hannu da dukkan masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da doka da Oda, don haka tana kira ga Al’umma, Malamai da ‘yan siyasa, shuwagabanni da Suyi wa’azuzzuka ko jawabai Da zasu tabbatar da zaman lafiya, samar da hadin kai, gami da wayar da kan mabiyan su hanyoyin da zasu kare kansu a yayin bukukuwan.
Wannan shi yafi dacewa kasancewar kada wasu suyi amfani da damar wajen tada zaune tsaye.
Hakazalika ‘yan siyasa a yayin da suke yakin neman zabe, ana so su gudanar cikin ka’ida, ya kamata su nisan ci labaran karya, kalaman kyama, tashin hankali da dukkan Abubuwan da zasu kassara tsaron kasa.
Haka kuma sanarwar ta bukaci ‘yan kasuwa dasu gujewa dabi’un da zasu haifar da hauhawar farashin maras fa’ida, kagar karancin samfuran kayayyaki abun da ka iya haifar da tashin hankali ta hanyar jifa Al’umma cikin halin rashin tabbas.
Hukumar ta kuma bukaci ‘yan Jarida da kungiyoyi masu zaman kansu da su kasance masu kishin kasa a yayin gudanar da ayyukan su matsayin su na masu ruwa da tsaki a fannin gina kasa da godabar da harkokin tsaron ta.
Daga Bisani shugaban Hukumar Alhaji Y. M Bichi, CFR, fwc a madadin jami’an hukumar yana Fatan Al’ummar zasu gudanar da bikin cikin kwanciyar hankali tare da tayasu murnar sabuwar shekara
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp