Home General Gwamnatin Jihar Kano Zata samar da Sabuwar Kwalejin koyar da harkokin Lafiya

Gwamnatin Jihar Kano Zata samar da Sabuwar Kwalejin koyar da harkokin Lafiya

Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar ya kaddamar da wani kwamiti da zai duba tare da yadda za’a samar da wata sabuwar Kwalegin koyar da harkokin kiwon lafiya domin magance matsalolin rashin Likitoci a kano da ma Nigeria baki daya.
Gwamna Ganduje ya kaddamar da kwamitin ne Mai mutane 19 yayin taron majalisar zartarwar ta jiha na wannnan makon wanda ya gudana a gidan gwamnatin jihar kano.
Ganduje ya bukaci yan kwamitin da su zage damtse wajen sauke nauyin da aka dora musu akan lokaci duba da muhimmanci da yadda al’ummar jihar kano ke bukatar Kwalegin saboda karacin jami’an lafiya da ake fama da su.
Ya ce an dorawa kwamitin Alhakin aikin tsara yadda za’a samar daga Kwalegin da inda za’a samar da ita da Kuma tabbatar da tsarin karantarwa a Kwalegin da dai sauransu.
Da yake jawabi bayan mika masa takardar shaidar kama aiki Shugaban kwamitin Farfesa Abdulsalam Nasidi ya ce an samar da kwamitin a lokacin daya dace, idan akai la’akari da yawan al’umma da kuma karancin jami’an kula da lafiya a Kano.
Ya kuma ce bada tabbacin zasu yi aiki kamar yadda ya kamata domin tabbatar da samar da Kwalegin, Inda yace zasu kammala aikin cikin wata guda kamar yadda Gwamnan ya bukata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp