NBA ta Umarci Gwamnatin Nijeriya ta gaggauta bin Umarni Kotu

Kungiyar lauyoyin Nijeriya ta NBA ta umarci gwamnatin tarayyar kasar da ta gaggauta bin umarnin kotun kolin kasar na kara wa’adin karbar tsoffin kudin data sauyawa fasali.

Shugaban kungiyar na kasa Yakubu Maikyau ne ya bayyana hakan ta cikin wata samara da ya fitar ranar litinin a kasar.

Wannan na zuwa ne tun bayan da kotun kolin kasar a ranar 3 ga watan maris ta bayar da umarnin a cigaba da karbar tsoffin kudin har zuwa 31 ga watan disambar 2023.

Tun bayan da kotun kolin da bayar da umarnin gwamantin tarayya kasar da babban bankin kasar na CBN basu fitar da sanarwa ga al’ummar kasar domin cigaba da amfani da tsofaffin takardun kudin ba.

Shugaban kungiyar lauyoyin ta NBA ya nuna matukar damuwar sa kan yadda sauyin kudin ya jefa al’ummar kasar cikin halin kakanakayi, inda yace yin watsi da hukuncin kotu da gwamantin tarayya kasar tayi ya nuna zagawar kundin tsarin mulkin kasar tare da damukradiyya.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 20 minutes 30 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 1 minute 55 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com