Home Labarai LP ta hade da PDP a jihar Katsina

LP ta hade da PDP a jihar Katsina

Shuwagabannin jam’iyyar Labour Party (LP) reshen jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya sun amince da marawa dan takarar gwamna karkashin inuwa jam’iyyar PDP a jihar, Sanata Yakubu Dan-marke.

Wakilan jam’iyyar bisa jagorancin mukaddashin shugaban jam’iyyar LP ta jihar, Kwamared Mannir Salisu ya jagoranta, ya ce matakin nasu na zuwa ne bayan shugaban jam’iyyar kuma dan takarar kujerar gwamnan jihar ya dangwarar da shahadar jami’yyar LP zuwa Jam’iyyar APC

A cewar Salisu, ’yan takarar da aka zabo daga unguwanni daban-daban, kananan hukumomi da Jihohi, sun cimma wannan matsayar ne bayan kammala shawarwarin da suka dace da nufin neman sahihin dan takara da zai kai jihar ga tudun mun tsira

Salisu yace ‘ya’yan jam’iyyar da suka fito daga mazabu da dama na jihar sun amince da matakin, haka kuma ya bukaci dukkan magoya bayan jam’iyyar Labour Party dake jihar ta katsina su yi fitar farin dango a ranar 18 ga watan maris su kada kur’aun su ga Jam’iyyar PDP mai alamar laima.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp