Home Labarai LP ta hade da PDP a jihar Katsina

LP ta hade da PDP a jihar Katsina

Shuwagabannin jam’iyyar Labour Party (LP) reshen jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya sun amince da marawa dan takarar gwamna karkashin inuwa jam’iyyar PDP a jihar, Sanata Yakubu Dan-marke.

Wakilan jam’iyyar bisa jagorancin mukaddashin shugaban jam’iyyar LP ta jihar, Kwamared Mannir Salisu ya jagoranta, ya ce matakin nasu na zuwa ne bayan shugaban jam’iyyar kuma dan takarar kujerar gwamnan jihar ya dangwarar da shahadar jami’yyar LP zuwa Jam’iyyar APC

A cewar Salisu, ’yan takarar da aka zabo daga unguwanni daban-daban, kananan hukumomi da Jihohi, sun cimma wannan matsayar ne bayan kammala shawarwarin da suka dace da nufin neman sahihin dan takara da zai kai jihar ga tudun mun tsira

Salisu yace ‘ya’yan jam’iyyar da suka fito daga mazabu da dama na jihar sun amince da matakin, haka kuma ya bukaci dukkan magoya bayan jam’iyyar Labour Party dake jihar ta katsina su yi fitar farin dango a ranar 18 ga watan maris su kada kur’aun su ga Jam’iyyar PDP mai alamar laima.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp