Home Labarai LP ta hade da PDP a jihar Katsina

LP ta hade da PDP a jihar Katsina

Shuwagabannin jam’iyyar Labour Party (LP) reshen jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya sun amince da marawa dan takarar gwamna karkashin inuwa jam’iyyar PDP a jihar, Sanata Yakubu Dan-marke.

Wakilan jam’iyyar bisa jagorancin mukaddashin shugaban jam’iyyar LP ta jihar, Kwamared Mannir Salisu ya jagoranta, ya ce matakin nasu na zuwa ne bayan shugaban jam’iyyar kuma dan takarar kujerar gwamnan jihar ya dangwarar da shahadar jami’yyar LP zuwa Jam’iyyar APC

A cewar Salisu, ’yan takarar da aka zabo daga unguwanni daban-daban, kananan hukumomi da Jihohi, sun cimma wannan matsayar ne bayan kammala shawarwarin da suka dace da nufin neman sahihin dan takara da zai kai jihar ga tudun mun tsira

Salisu yace ‘ya’yan jam’iyyar da suka fito daga mazabu da dama na jihar sun amince da matakin, haka kuma ya bukaci dukkan magoya bayan jam’iyyar Labour Party dake jihar ta katsina su yi fitar farin dango a ranar 18 ga watan maris su kada kur’aun su ga Jam’iyyar PDP mai alamar laima.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp