NDLEA ta tabbatar da gyara shafinta na daukar aiki

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA ta tabbatawar wa ‘yan Nijeriya dake neman aiki a hukumar cewa ta shawo kan matsalar da ake fuskanta a shafinta na daukar aiki da nufin ganin an sami mafita daga yanzu zuwa ko wanne lokaci.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran hukumar Femi babafemi ya fitar, mai dauke da kwanan wata 15 ga watan Maris 2023. Inda yace sa’oi kadan da bude shafin a ranar lahadi 12 ga wata Maris, ya fara samun tangarda sakamakon yadda mutane sama da dubu 200 ke kokarin cike takardar samun gurbin aiki a hukumar.

Domin warware wannan matsalar hukumar a ranar talata 14 ga watan Maris ta inganta shafin domin daukar dimbin masu bukatar samun gurbin aiki a hakumar bayan da sama da mutane 53,170 suka nasara shiga tashin.

A halin yanzu, shafin yana aiki yadda ya kamata. Don haka hukumar na amfani da wannan dama wajen neman afuwar wadanda suka bibiyi shafin bisa tsaikon da suka samu da su kara hakuri.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 38 minutes 55 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 20 minutes 20 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com