Home Labarai NDLEA ta tabbatar da gyara shafinta na daukar aiki

NDLEA ta tabbatar da gyara shafinta na daukar aiki

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA ta tabbatawar wa ‘yan Nijeriya dake neman aiki a hukumar cewa ta shawo kan matsalar da ake fuskanta a shafinta na daukar aiki da nufin ganin an sami mafita daga yanzu zuwa ko wanne lokaci.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran hukumar Femi babafemi ya fitar, mai dauke da kwanan wata 15 ga watan Maris 2023. Inda yace sa’oi kadan da bude shafin a ranar lahadi 12 ga wata Maris, ya fara samun tangarda sakamakon yadda mutane sama da dubu 200 ke kokarin cike takardar samun gurbin aiki a hukumar.

Domin warware wannan matsalar hukumar a ranar talata 14 ga watan Maris ta inganta shafin domin daukar dimbin masu bukatar samun gurbin aiki a hakumar bayan da sama da mutane 53,170 suka nasara shiga tashin.

A halin yanzu, shafin yana aiki yadda ya kamata. Don haka hukumar na amfani da wannan dama wajen neman afuwar wadanda suka bibiyi shafin bisa tsaikon da suka samu da su kara hakuri.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp