Rahotanni daga Nijeriya na bayyana cewa Mutane 214 ne suka mutu tsakanin watan Janairu da Maris din shekarar 2023, a hare-haren ‘yan bindiga da rikicin ƙabilanci da hare-haren ɗaukar fansa a jihar Kaduna a Najeriya.

A cikin wannan adadi 14 mata ne a yayin da huɗu yara ne ‘yan ƙasa da shekaru 18.

A gundumar Kaduna ta Tsakiya, an samu rahoton mutuwar mutane 115 (kashi 54 bisa dari na yawan adadin).

Ɗari da takwas na waɗannan adadi sun faru ne a yankunan ƙananan hukumomin Birnin Gwari, da Giwa, da Igabi, Chikun da kuma Kajuru.

Ƙananan hukumomi Giwa da Birnin Gwari duka sun samu yawan adadin mutane 32 da suka mutu, karamar hukumar Chikun 25, Igabi 13, sai Kajuru shida a watannin ukun farkon shekarar 2023.

A yankin kudancin Kaduna an samu mutuwar mutane 61 a daidai irin wannan lokaci.

Yanayin kai hare-hare da na daukar fansa, da munanan tashe-tashen hankula na addini da na kabilanci – tsakanin hare-haren ‘yan bindiga – sun faru a karamar hukumar Zangon Kataf, inda mutane 19 suka rasa rayukansu.

Mutane 12 ne kuma aka kashe a ƙaramar hukumar Sanga a cikin watanni ukun farko na shekarar 2023.

Yankin arewacin jihar ya shaida mutuwar mutane 38 a watanni ukun farko, inda aka samu mutuwar mutane 22 a karamar hukumar Zaria.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp