Mutum miliyan 4.3 za su yi fama da yunwa a jihohin Adamawa, Borno da Yobe – MDD

Shirin Majalisar Ɗinkin Duniya na samar da abinci ya yi gargaɗin cewa akwai mutum miliyan 4.3 za su yi fama da matsananciyar yunwa a jihohin Adamawa da Borno da kuma Yobe, dukkansu a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Shirin ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar, game da wani rahoto da ya tattara kan matsananciyar yunwa a yankin ƙasashen kudu da hamadar Sahara.

Shirin na WFP ya nuna damuwa kan rikicin da aka kwashe shekaru ana yi da ‘yan bindiga zai iya jefa Najeriya cikin yunwa da tamowa, yayin da miliyoyin mutane suka dogara kan taimako da ake ba su na abinci, wanda kuma suke fuskantar barazanar faɗawa cikin yunwa.

“Kimanin mutum 600,000 na kan gabar faɗawa cikin wannan musifa.

Mutane za su fuskanci yanayin neman ɗaukin gaggawa saboda ƙarancin abinci, za kuma a fuskanci mummunar matsalar tamowa da mace-mace saboda ƙarancin kai kayan agaji,” in ji shirin.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 47 minutes 11 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 28 minutes 36 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com