Home Labarai Mutum miliyan 4.3 za su yi fama da yunwa a jihohin Adamawa,...

Mutum miliyan 4.3 za su yi fama da yunwa a jihohin Adamawa, Borno da Yobe – MDD

Shirin Majalisar Ɗinkin Duniya na samar da abinci ya yi gargaɗin cewa akwai mutum miliyan 4.3 za su yi fama da matsananciyar yunwa a jihohin Adamawa da Borno da kuma Yobe, dukkansu a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Shirin ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar, game da wani rahoto da ya tattara kan matsananciyar yunwa a yankin ƙasashen kudu da hamadar Sahara.

Shirin na WFP ya nuna damuwa kan rikicin da aka kwashe shekaru ana yi da ‘yan bindiga zai iya jefa Najeriya cikin yunwa da tamowa, yayin da miliyoyin mutane suka dogara kan taimako da ake ba su na abinci, wanda kuma suke fuskantar barazanar faɗawa cikin yunwa.

“Kimanin mutum 600,000 na kan gabar faɗawa cikin wannan musifa.

Mutane za su fuskanci yanayin neman ɗaukin gaggawa saboda ƙarancin abinci, za kuma a fuskanci mummunar matsalar tamowa da mace-mace saboda ƙarancin kai kayan agaji,” in ji shirin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp