Home DUNIYA Sama da mutane dubu 800 za su gudu daga Sudan- MDD

Sama da mutane dubu 800 za su gudu daga Sudan- MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta ce sama da mutane dubu 800 ne ake sa ran za su tsere daga Sudan sakamakon kazamin rikicin da ake yi tsakanin rundunar sojin kasar da dakarun Kai Daukin Gaggawa na RSF.

Wani babban jami’in Majalisar Dinkin Duniya, Raouf Mazou ne ya bayyana haka a Geneva, ina yake cewa idan ba a warware wannan rikici da wuri ba, za a ci gaba da samun dimbim mutanen da ke arcewa daga Sudan don neman mafaka da agaji.

Saboda haka ya ce a tattaunawar da suka yi da hukumomin da wannan lamari zai shafa, sun cimma matsayar shirya wa mutane dubu 815 da ake sa ran za su iya arcewa zuwa kasashe 7 da ke makwaftaka da Sudan.

Wannan hasashe da aka yi, in ji Mazou ya hada da kimanin ‘yan kasar Sudan dubu 580 da kuma wadanda ke gudun hijira a halin yanzu daga Sudan ta Kudu da wasu wuraren.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp