Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin rage radadi ga ‘yan kasa

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin ragewa ‘yan Najeriya radadin cire tallafin man fetur ta hanyar bunkasa bangarorin sufuri, da ababen more rayuwa, da ilimi, da samar da dawwamammen hasken wuta lantarki, da kuma inganta bangaren lafiya.

Shugaba Tinubu yayi wannan alwashi ne lokacin dayake jawabi ga ‘yan Najeriya akan zagayowar ranar dimokradiyya.

Mista Tinubu yacigaba da cewa, ” A ranar demokradiiya ta wannan shekara, Ina kira garemu da mukara sadaukar da kanmu domin karfafa wannan tsari na gwamnati daya baiwa kowa ‘yancinsa, wanda hakan kuma shine tsarinmu tsawon wadannan shekaru 24 da dawowar mulkin demokradiiya.”

A ranar 29 ga watan mayu lokacin dayake jawabi bayan amsar rantsuwa, Shugaba Tinubu yabayyana cire tallafin mai kacokan lamarin daya saka al’ummar kasar cikin rudani biyo bayan tashin gouron zabi da farashin mai da sauran kayan masarufi sukayi a fadin kasar.

Shugaba Tinubu yayi allawarin tabbatar da bai baiwa ‘yan Najeriya kunya ba, tahanyar cika alkawurran daya dauka lokacin yakin neman zabe.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 32 minutes 58 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 14 minutes 23 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com