Home Labarai Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin rage radadi ga ‘yan kasa

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin rage radadi ga ‘yan kasa

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yayi alkawarin ragewa ‘yan Najeriya radadin cire tallafin man fetur ta hanyar bunkasa bangarorin sufuri, da ababen more rayuwa, da ilimi, da samar da dawwamammen hasken wuta lantarki, da kuma inganta bangaren lafiya.

Shugaba Tinubu yayi wannan alwashi ne lokacin dayake jawabi ga ‘yan Najeriya akan zagayowar ranar dimokradiyya.

Mista Tinubu yacigaba da cewa, ” A ranar demokradiiya ta wannan shekara, Ina kira garemu da mukara sadaukar da kanmu domin karfafa wannan tsari na gwamnati daya baiwa kowa ‘yancinsa, wanda hakan kuma shine tsarinmu tsawon wadannan shekaru 24 da dawowar mulkin demokradiiya.”

A ranar 29 ga watan mayu lokacin dayake jawabi bayan amsar rantsuwa, Shugaba Tinubu yabayyana cire tallafin mai kacokan lamarin daya saka al’ummar kasar cikin rudani biyo bayan tashin gouron zabi da farashin mai da sauran kayan masarufi sukayi a fadin kasar.

Shugaba Tinubu yayi allawarin tabbatar da bai baiwa ‘yan Najeriya kunya ba, tahanyar cika alkawurran daya dauka lokacin yakin neman zabe.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp