Jihohi 14 da zasu fuskanci Ambaliyar Ruwa a Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta fitar da sanarwar hasashen ambaliya a shekara ta 2023, inda ta ce jihohi 14 da al’ummomi 31 za su iya ganin ruwan sama kamar da bakin kwarya da zai iya haifar da ambaliya daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuli.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ma’aikatar kula da muhalli ta tarayya ta fitar.

A cewar sanarwar, an gano jihohin da al’ummomin da suka hada da:

Plateau – Langtang, Shendam

Kano – Sumaila, Tudun Wada

Sokoto – Shagari, Goronyo da Silame

Delta – Okwe

Kaduna – Kachia

Akwa Ibom – Upenekang

Adamawa – Mubi, Demsa, Song, Mayo-Belwa, Jimeta, Yola

Katsina – Katsina, Jibia, Kaita da Bindawa

Kebbi – Wara, Yelwa da Gwandu

Zamfara – Shinkafi, Gummi

Borno – Briyel

Jigawa – Gwaram

Kwara – Jebba

Niger – Mashegu, Kontagora

Gwamnatin ta kuma bukaci masu ruwa da tsaki a jihohin da abin ya shafa da su dauki matakan kariya domin kiyaye asarar rayuka da dukiyoyi.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 11 minutes 59 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 53 minutes 24 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com