Home Labarai Jihohi 14 da zasu fuskanci Ambaliyar Ruwa a Nijeriya

Jihohi 14 da zasu fuskanci Ambaliyar Ruwa a Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta fitar da sanarwar hasashen ambaliya a shekara ta 2023, inda ta ce jihohi 14 da al’ummomi 31 za su iya ganin ruwan sama kamar da bakin kwarya da zai iya haifar da ambaliya daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuli.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ma’aikatar kula da muhalli ta tarayya ta fitar.

A cewar sanarwar, an gano jihohin da al’ummomin da suka hada da:

Plateau – Langtang, Shendam

Kano – Sumaila, Tudun Wada

Sokoto – Shagari, Goronyo da Silame

Delta – Okwe

Kaduna – Kachia

Akwa Ibom – Upenekang

Adamawa – Mubi, Demsa, Song, Mayo-Belwa, Jimeta, Yola

Katsina – Katsina, Jibia, Kaita da Bindawa

Kebbi – Wara, Yelwa da Gwandu

Zamfara – Shinkafi, Gummi

Borno – Briyel

Jigawa – Gwaram

Kwara – Jebba

Niger – Mashegu, Kontagora

Gwamnatin ta kuma bukaci masu ruwa da tsaki a jihohin da abin ya shafa da su dauki matakan kariya domin kiyaye asarar rayuka da dukiyoyi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp