Home Labarai Faifen Bidiyon Ganduje na Dollar Gaskiya ne- Muhy

Faifen Bidiyon Ganduje na Dollar Gaskiya ne- Muhy

Kwararru masu binciken kwakwaf sun tabbatar da sahihancin faifen bidiyon da ke nuna tsohon gwamnan jihar Kano Dafta Abdullahi Umar Ganduje na cusa daloli a aljihunsa da aka ce cin hanci ne ya karba daga hannun wasu ‘yan kwangila.

Shugaban Hukumar Sauraren Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin hanci ta Jihar Kano Muhyi Magaji Rimin Gado ne ya bayyana hakan a wani taron yini guda kan yaki da cin hanci da rashawa a jihar.

Ta cikin jawabin nasa Muhyi ya ce, an tabbatar da sahihancin faya-fayan bidiyon.

Inda yace tun lokacin da aka saki hotunan bidiyon, jama’a ke ta kalubalantar hukumar da ta wanke gwamnan daga wannan zargi  ko kuma akasin haka.

A shekarar 2017, Jaridar Daily Nigerian da ake wallafawa a yanar gizo ta saki wasu hotunan bidiyon Ganduje na karbar kudadden da ake zargin cewa, na cin hanci ne, al’amarin da ya haddasa cece-kuce a ciki da wajen jihar.

Muhyi ya ce, tun a shekarar 2018 ne suka kaddamar da bincike kan lamarin, amma suka gaza zurfafa binciken Gandujen saboda a lokacin saboda rigar kariya da yake da ita a matsayinsa na gwamna.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp