Home Labarai Faifen Bidiyon Ganduje na Dollar Gaskiya ne- Muhy

Faifen Bidiyon Ganduje na Dollar Gaskiya ne- Muhy

Kwararru masu binciken kwakwaf sun tabbatar da sahihancin faifen bidiyon da ke nuna tsohon gwamnan jihar Kano Dafta Abdullahi Umar Ganduje na cusa daloli a aljihunsa da aka ce cin hanci ne ya karba daga hannun wasu ‘yan kwangila.

Shugaban Hukumar Sauraren Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin hanci ta Jihar Kano Muhyi Magaji Rimin Gado ne ya bayyana hakan a wani taron yini guda kan yaki da cin hanci da rashawa a jihar.

Ta cikin jawabin nasa Muhyi ya ce, an tabbatar da sahihancin faya-fayan bidiyon.

Inda yace tun lokacin da aka saki hotunan bidiyon, jama’a ke ta kalubalantar hukumar da ta wanke gwamnan daga wannan zargi  ko kuma akasin haka.

A shekarar 2017, Jaridar Daily Nigerian da ake wallafawa a yanar gizo ta saki wasu hotunan bidiyon Ganduje na karbar kudadden da ake zargin cewa, na cin hanci ne, al’amarin da ya haddasa cece-kuce a ciki da wajen jihar.

Muhyi ya ce, tun a shekarar 2018 ne suka kaddamar da bincike kan lamarin, amma suka gaza zurfafa binciken Gandujen saboda a lokacin saboda rigar kariya da yake da ita a matsayinsa na gwamna.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp