Home Labarai Zamu kare Damukradiyya a Nijeriya – Sojojin Nijeriya

Zamu kare Damukradiyya a Nijeriya – Sojojin Nijeriya

Babban hafsan sojin Najeriya Laftanar Janar Taoreed Lagbaja ya ce babban abin da ya fi dacewa da ƙasar a wannan zamani shi ne mulkin dimokradiyya.

Babban hafsan sojin ya bayyana haka ne a lokacin bikin yaye manyan sojoji da aka gudanar da makarantar yaye manyan hafsoshi ta Jaji da ke Kaduna, kamar yadda wata sanarwa da kakakin rundunar Burgediya Janar Onyema Nwachukwu ya fitar.

Laftanar Janar Lagbaja ya ce dole ne a tunasar da sojojin ƙasar cewa taimakonsu wajen tabbatuwa da ɗorewar mulki shi ne babbar hanyar nuna ƙwarewa a aikin soji.

Ya kuma ce babban burin kowanne ɗan Najeriya a yanzu shi ne ɗorewar mulkin dimokradiyya, wanda zai tabbatar da haɗin kan ƙasa da kuma kare muradun ‘yan Najeriya, ba tare da la’akari da bambanci addini ko na ƙabila ba.

”A don haka ina kira ga duka sojojin Najeriya su bayar da gudunmowarsu wajen tabbatar da ɗorewar mulkin dimokraɗiyya, sannan su kauce wa shiga lamuran siyasa a lokacin gudanar da ayyukansu”, in babban hafsan sojojin.

Ya kuma jaddada burin rundunar sojin ƙasar na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ƙasar.

Laftanar Janar Lagbaja ya ce sojojin ƙasar tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaron ƙasar na aiki ba dare ba rana domin tabbatar da kare martabar ƙasar.

Babban hafsan sojin na wannan jawabi ne a daidai lokacin da ƙasashen ƙungiyar Ecowas suka bai wa sojojin da suka hamɓarar da gwamnatin farar hula ta Mohamed Bazoum a Nijar wa’adin mako guda na su mayar da shi kan mulki su fuskanci tarin takunkumai, ciki har da na matakin Soji.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp