KAROTA zata dauki mataki kan masu zaluntar Jami’anta a Kano

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta jihar Kano KAROTA ta ce za ta bi kadin abinda wasu bata-gari suka yi wa jami’anta a karshen makon da ya gabata

Shugaban Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta jiha KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka ta cikin wata takardar manema labarai da kakakin hukumar Nabilusi Abubakar Na’isa ya fitar mai dauke da kwanan watan 31/10.2023 aka kuma raba ga manema labarai a jihar Kano.

Yayin da yake duba biyu daga cikin jami’an  hukumar da ke kwance a asibitin Murtala da asibitin Kashi na Dala, Shugaban ya ce, ba zai zuba ido ya bari ana cin zarafin jami’an ba, a don haka ya bayar da tabbacin mika lamarin wajen jami’an ‘Yan Sanda domin fadada bincike tare da daukar matakin da ya kamata.

Haka Kuma, Tawagar shugaban Hukumar ta kai ziyarar Ta’aziyya ga jami’inta mai suna Nasiru Sani Abubakar a unguwar Yakasai Wanda Allah ya yi wa rasuwa sakamakon bige shi da mota ta yi; Ya yi Ta’aziyya ga iyalan jami’in tare da adduar samun gafara a gare shi da sauran alumma gaba daya.

Daga bias ya ja hankalin jami’an Hukumar da su ci gaba da gudanar da aikin su cikin kwarewa da mutunta jama’a.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 13 minutes 29 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 54 minutes 54 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com