Home Labarai KAROTA zata dauki mataki kan masu zaluntar Jami’anta a Kano

KAROTA zata dauki mataki kan masu zaluntar Jami’anta a Kano

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta jihar Kano KAROTA ta ce za ta bi kadin abinda wasu bata-gari suka yi wa jami’anta a karshen makon da ya gabata

Shugaban Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta jiha KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka ta cikin wata takardar manema labarai da kakakin hukumar Nabilusi Abubakar Na’isa ya fitar mai dauke da kwanan watan 31/10.2023 aka kuma raba ga manema labarai a jihar Kano.

Yayin da yake duba biyu daga cikin jami’an  hukumar da ke kwance a asibitin Murtala da asibitin Kashi na Dala, Shugaban ya ce, ba zai zuba ido ya bari ana cin zarafin jami’an ba, a don haka ya bayar da tabbacin mika lamarin wajen jami’an ‘Yan Sanda domin fadada bincike tare da daukar matakin da ya kamata.

Haka Kuma, Tawagar shugaban Hukumar ta kai ziyarar Ta’aziyya ga jami’inta mai suna Nasiru Sani Abubakar a unguwar Yakasai Wanda Allah ya yi wa rasuwa sakamakon bige shi da mota ta yi; Ya yi Ta’aziyya ga iyalan jami’in tare da adduar samun gafara a gare shi da sauran alumma gaba daya.

Daga bias ya ja hankalin jami’an Hukumar da su ci gaba da gudanar da aikin su cikin kwarewa da mutunta jama’a.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp