Home Labarai CBN ya musanta sake fasalin kudin Nijeriya

CBN ya musanta sake fasalin kudin Nijeriya

Babban Bankin Najeriya ya ce ba shi da wani shiri na sake kirkiro sabbin takardun naira a shekara mai zuwa.

Wata sanarwa da daraktan sadarwa na Bankin Najeriya, Isa Abdulmumin ya fitar ranar Talata, ta bukaci ‘yan Najeriya su yi watsi da wani takaitaccen sakon waya da ake yadawa, wanda ke nuna cewa CBN na shirin sake bullo da sabbin takardun naira a shekara ta 2024. Takardar sanarwa ta bayyana cewa sakon ba haka yake ba.

“Mun shiga damuwa game da wannan batu, wanda muka musanta tun ba yanzu ba, amma ga alama yana samun karbuwa da muhawara masu yawa a kan illar irin wannan manufa ga tattalin arzikin Najeriya.

CBN ya ce “Muna son jaddada cewa bayanin da ke cikin wannan sako, ba haka yake ba”. Ya kara da cewa masu wallafa sako a yunkurinsu na jamhuru, sun jirkita rubutun daga wata tsohuwar manufa ta gwamnan CBN na baya a shekara ta 2007, amma sai suke bayyana shi tamkar yanzu ya faru.

Ya dai nanata cewa a yanzu babu wani shiri na sake fasalin takardun kudin kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp