Home Labarai KAROTA zata dauki mataki kan masu zaluntar Jami’anta a Kano

KAROTA zata dauki mataki kan masu zaluntar Jami’anta a Kano

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta jihar Kano KAROTA ta ce za ta bi kadin abinda wasu bata-gari suka yi wa jami’anta a karshen makon da ya gabata

Shugaban Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta jiha KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka ta cikin wata takardar manema labarai da kakakin hukumar Nabilusi Abubakar Na’isa ya fitar mai dauke da kwanan watan 31/10.2023 aka kuma raba ga manema labarai a jihar Kano.

Yayin da yake duba biyu daga cikin jami’an  hukumar da ke kwance a asibitin Murtala da asibitin Kashi na Dala, Shugaban ya ce, ba zai zuba ido ya bari ana cin zarafin jami’an ba, a don haka ya bayar da tabbacin mika lamarin wajen jami’an ‘Yan Sanda domin fadada bincike tare da daukar matakin da ya kamata.

Haka Kuma, Tawagar shugaban Hukumar ta kai ziyarar Ta’aziyya ga jami’inta mai suna Nasiru Sani Abubakar a unguwar Yakasai Wanda Allah ya yi wa rasuwa sakamakon bige shi da mota ta yi; Ya yi Ta’aziyya ga iyalan jami’in tare da adduar samun gafara a gare shi da sauran alumma gaba daya.

Daga bias ya ja hankalin jami’an Hukumar da su ci gaba da gudanar da aikin su cikin kwarewa da mutunta jama’a.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp