Home DUNIYA Jamhuriyyar Nijar zata fara sayar da Man fetur ga kasashen duniya

Jamhuriyyar Nijar zata fara sayar da Man fetur ga kasashen duniya

Shuwagabannin mulkin sojin Nijar sun kaddamar da wani babban batutun man fetur da zai riƙa tura ɗanyen mai daga ƙasar zuwa Jamhuriyar Benin, mai maƙwabtaka da kasar.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya bayyana cewa gidan talabijin na ƙasar ne ya ambata aiki, wanda ke da tsawon kusan kilomita 2,000 da zai bai wa Nijar damar sayar da ɗanyen man fetur da take haƙowa a kasuwannin duniya a karon farko, ta hanyar amfani da mashigar ruwan Seme da ke Benin.

An gudanar da bikin ƙaddamar da aikin cibiyar haƙo man fetur ta Agadem, mai nisan kilomita 1,700 daga Yamai baban birnin ƙasar.

Firaministan Nijar, Ali Mahaman Lamine, ya ce za a yi amfani da kuɗin da aka samu daga cinikin man fetur din “don tabbatar da tsaro da ci gaban ƙasarmu”.

Kan iyakar Nijar da Jamhuriyar Benin ta kasance a rufe sakamakon jerin takunkuman da ƙungiyar Ecowas ta saka wa Nijar bayan juyin mulkin ranar 26 ga watan Yuli.

Wakilai daga ma’aikatun makamashin ƙasashen Mali da Burkina Faso – waɗanda ke nuna goyon bayansu ga sabuwar gwamnatin sojin Nijar – sun halarcin bikin ƙaddamar da aikin.

An tsara kammala aikin a shakerar 2022, to amma annobar korona ta haddasa jinkirin aikin, kamar yadda masu gudanar da aikin suka shada wa AFP. Kamfanin man Fetur na Ƙasar China, (CNPC) ne ke aikin haƙo man.

Gwamnatin Nijar ta ce aikin ya laƙume dala biliyan shida, ciki har da dala biliyan huɗu na gina wuraren man, da kuma dala biliyan 2.3 na aikin shimfiɗa bututun man.

Ta ƙara da cewa wannan aiki zai bai wa ƙasar damar ƙara yawan man da take haƙowa zuwa ganga 110,000 a kowace rana, da nufin ƙara shi zuwa 200,000 a kowace rana zuwa shekarar 2026.

Ƙasar Nijar – wadda sojoji suka kifar da gwamnatin farar hula cikin wata Yuli – ta fuskanci jerin zanga-zanga da kiraye-kirayen ficewar sojojin Faransa daga ƙasar.

Ga kuma jerin takunkumai daga ƙungiyar Ecowas, sannan ƙasashen Yamma da dama sun yanke tallafin da suke ba ta.

Bankin duniya ya yi gargaɗin cewa arzikin da ake samu a cikin ƙasar na iya raguwa da kashi 2.3 a wannan shekara matuƙar ba ɗage mata takunkuman ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp