Home Labarai Dakarun sojoji sun jikkata sananne dan ta’addan Dogo Gide

Dakarun sojoji sun jikkata sananne dan ta’addan Dogo Gide

Wani rahoton binciken jaridar PRNigeria ya tabbatar mata da cewa dakarun soojin Nijeriya sun sami nasarar raunata Dogo gide, dan ta’addan da ake nema ruwa a Jallo a jihar Zamfara.
Dogo gide ya tsallake rijiya da baya, da raunikan harbin bindiga a jikin sa, bayan wani hari da dakarun soji suka kai a wani bangare na kakkabe maboyar ‘yan ta’addan dake jihar Zamfara.
Wata majiya daga rundunar ta tabbatarwa da PRNigeria cewa sojojin sun tarwatsa maboyar ‘yan ta’addan dake na jihar dake kauyukan Dansadau, Mai Tukunya da Babban Doka.
“Yayin gudanar da atisayen dakarun sun mamaye yankin Ya’u Sarkin Pawa gida Dogo Gode, inda suka bincika gidan suka kuma tarwatsa shi.
“An sami kayayyaki a gidan Dogo Gide, da suka hadar da kayan dinka kayayyakin sawa na sojoji da sauran jami’an tsaro, kayan fashewa na (IEDs); wani karamin wurin shan magani domin bayar da taimakon gaggawa ga ‘yan bindiga, baburan hawa guda 5 da kekunan dinky, wanda duk dakarun suka bankawa wuta.
“Dakarun karkashin OPHD sun kuma sami nasarar tarwatsa ‘yan ta’addan dake kauyukan Malele, Mutunji, Kwana, Kamatso, Kememe, Kango wanda ke matsayin maboya ga ‘yan ta’addan.
“haka kuma sojojin sun bankado gami da tarwatsa maboyar ‘yan bindigar a kauyukan Koli, Bakin Dutse da Farin Ruwa inda suka sami nasarar kwato Baburan hawa da wayoyin hannun guda 4” kamar yadda majiyar ta tabbatar.
PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp