Home Labarai Dakarun sojoji sun jikkata sananne dan ta’addan Dogo Gide

Dakarun sojoji sun jikkata sananne dan ta’addan Dogo Gide

Wani rahoton binciken jaridar PRNigeria ya tabbatar mata da cewa dakarun soojin Nijeriya sun sami nasarar raunata Dogo gide, dan ta’addan da ake nema ruwa a Jallo a jihar Zamfara.
Dogo gide ya tsallake rijiya da baya, da raunikan harbin bindiga a jikin sa, bayan wani hari da dakarun soji suka kai a wani bangare na kakkabe maboyar ‘yan ta’addan dake jihar Zamfara.
Wata majiya daga rundunar ta tabbatarwa da PRNigeria cewa sojojin sun tarwatsa maboyar ‘yan ta’addan dake na jihar dake kauyukan Dansadau, Mai Tukunya da Babban Doka.
“Yayin gudanar da atisayen dakarun sun mamaye yankin Ya’u Sarkin Pawa gida Dogo Gode, inda suka bincika gidan suka kuma tarwatsa shi.
“An sami kayayyaki a gidan Dogo Gide, da suka hadar da kayan dinka kayayyakin sawa na sojoji da sauran jami’an tsaro, kayan fashewa na (IEDs); wani karamin wurin shan magani domin bayar da taimakon gaggawa ga ‘yan bindiga, baburan hawa guda 5 da kekunan dinky, wanda duk dakarun suka bankawa wuta.
“Dakarun karkashin OPHD sun kuma sami nasarar tarwatsa ‘yan ta’addan dake kauyukan Malele, Mutunji, Kwana, Kamatso, Kememe, Kango wanda ke matsayin maboya ga ‘yan ta’addan.
“haka kuma sojojin sun bankado gami da tarwatsa maboyar ‘yan bindigar a kauyukan Koli, Bakin Dutse da Farin Ruwa inda suka sami nasarar kwato Baburan hawa da wayoyin hannun guda 4” kamar yadda majiyar ta tabbatar.
PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp