Home Labarai Dakarun sojoji sun jikkata sananne dan ta’addan Dogo Gide

Dakarun sojoji sun jikkata sananne dan ta’addan Dogo Gide

Wani rahoton binciken jaridar PRNigeria ya tabbatar mata da cewa dakarun soojin Nijeriya sun sami nasarar raunata Dogo gide, dan ta’addan da ake nema ruwa a Jallo a jihar Zamfara.
Dogo gide ya tsallake rijiya da baya, da raunikan harbin bindiga a jikin sa, bayan wani hari da dakarun soji suka kai a wani bangare na kakkabe maboyar ‘yan ta’addan dake jihar Zamfara.
Wata majiya daga rundunar ta tabbatarwa da PRNigeria cewa sojojin sun tarwatsa maboyar ‘yan ta’addan dake na jihar dake kauyukan Dansadau, Mai Tukunya da Babban Doka.
“Yayin gudanar da atisayen dakarun sun mamaye yankin Ya’u Sarkin Pawa gida Dogo Gode, inda suka bincika gidan suka kuma tarwatsa shi.
“An sami kayayyaki a gidan Dogo Gide, da suka hadar da kayan dinka kayayyakin sawa na sojoji da sauran jami’an tsaro, kayan fashewa na (IEDs); wani karamin wurin shan magani domin bayar da taimakon gaggawa ga ‘yan bindiga, baburan hawa guda 5 da kekunan dinky, wanda duk dakarun suka bankawa wuta.
“Dakarun karkashin OPHD sun kuma sami nasarar tarwatsa ‘yan ta’addan dake kauyukan Malele, Mutunji, Kwana, Kamatso, Kememe, Kango wanda ke matsayin maboya ga ‘yan ta’addan.
“haka kuma sojojin sun bankado gami da tarwatsa maboyar ‘yan bindigar a kauyukan Koli, Bakin Dutse da Farin Ruwa inda suka sami nasarar kwato Baburan hawa da wayoyin hannun guda 4” kamar yadda majiyar ta tabbatar.
PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp