Home Labarai Dakarun sojoji sun jikkata sananne dan ta’addan Dogo Gide

Dakarun sojoji sun jikkata sananne dan ta’addan Dogo Gide

Wani rahoton binciken jaridar PRNigeria ya tabbatar mata da cewa dakarun soojin Nijeriya sun sami nasarar raunata Dogo gide, dan ta’addan da ake nema ruwa a Jallo a jihar Zamfara.
Dogo gide ya tsallake rijiya da baya, da raunikan harbin bindiga a jikin sa, bayan wani hari da dakarun soji suka kai a wani bangare na kakkabe maboyar ‘yan ta’addan dake jihar Zamfara.
Wata majiya daga rundunar ta tabbatarwa da PRNigeria cewa sojojin sun tarwatsa maboyar ‘yan ta’addan dake na jihar dake kauyukan Dansadau, Mai Tukunya da Babban Doka.
“Yayin gudanar da atisayen dakarun sun mamaye yankin Ya’u Sarkin Pawa gida Dogo Gode, inda suka bincika gidan suka kuma tarwatsa shi.
“An sami kayayyaki a gidan Dogo Gide, da suka hadar da kayan dinka kayayyakin sawa na sojoji da sauran jami’an tsaro, kayan fashewa na (IEDs); wani karamin wurin shan magani domin bayar da taimakon gaggawa ga ‘yan bindiga, baburan hawa guda 5 da kekunan dinky, wanda duk dakarun suka bankawa wuta.
“Dakarun karkashin OPHD sun kuma sami nasarar tarwatsa ‘yan ta’addan dake kauyukan Malele, Mutunji, Kwana, Kamatso, Kememe, Kango wanda ke matsayin maboya ga ‘yan ta’addan.
“haka kuma sojojin sun bankado gami da tarwatsa maboyar ‘yan bindigar a kauyukan Koli, Bakin Dutse da Farin Ruwa inda suka sami nasarar kwato Baburan hawa da wayoyin hannun guda 4” kamar yadda majiyar ta tabbatar.
PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp